Harbin masu zanga zanga a Lekki: Gwamna Sanwo-Olu ya roƙi yafiyar ƴan Legas

Harbin masu zanga zanga a Lekki: Gwamna Sanwo-Olu ya roƙi yafiyar ƴan Legas

- Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya ba mutanen Lagas hakuri cewa su tona su binne domin wanzuwar zaman lafiya

- A wani jawabi a jihar gwamnan ya bayar da hakuri a kan bude wutar da aka yi wa masu zanga-zanga a kofar shiga Lekki

- Sai dai, Sanwo-Olu ya bayyana cewa babu wanda ya mutu a yayin bude wutar sabanin yadda ake ta yayatawa

Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya ba mazauna jihar Lagas hakuri sakamakon wuta da jami’an tsaro suka budewa masu zanga-zangar lumana a yankin Lekki a ranar Talata, 20 ga watan Oktoba, wanda aka ce ya yi sanadiyar mutuwar wasu.

A wani jawabi na fadin jiha da ya yi a ranar Laraba, 21 ga watan Oktoba, wanda Legit.ng ta bibiya, Gwamna Sanwo-Olu ya roki fusatattun matasan da su bayar da damar dawo da zaman lafiya.

Gwamnan ya ci gaba da bayyana cewa wannan shine lokaci mafi muni a tarihin jihar da Najeriya baki daya.

Harbin masu zanga zanga a Lekki: Gwamna Sanwo-Olu ya roƙi yafiyar ƴan Legas
Harbin masu zanga zanga a Lekki: Gwamna Sanwo-Olu ya roƙi yafiyar ƴan Legas Hoto: @jidesanwoolu
Asali: Twitter

“Lagas, Ina mai bayar da hakuri a kan abunda ya faru, ina ba matasanmu hakuri, dan Allah ku bayar da damar samun zama lafiya. Kowani rai na da amfani.”

KU KARATA KUMA: An tsaurara matakan tsaro a Kaduna yayinda zanga-zanga ke yaduwa

A cewarsa, a lokacin da gwamati ta saka dokar ta baci na sa’o’i 24 a jihar Lagas kuma matasan suka take umurnin, babu wani shugaba na zanga-zangar da za a yi wa magana.

Yayinda yake wanke kansa daga harin rundunar sojin, Sanwo-Olu ya bayyana gudanarwar sojin a Lekki a matsayin abun bakin ciki.

Ya yi alkawarin gabatar da lamarin a gaban manya sannan kuma cewa zai nemi agajin Shugaban kasa a matsayinsa na kwamandan rundunar tsaro ta kasa.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa sabanin yadda aka yi ta yayatawa, ba a rasa rai ba.

“Ba a rasa rai ko guda ba kamar yadda ake ta yayatawa a soshiyal midiya... Mun zagaya asibitoci da wuraren ajiye gawa.”

A baya mun ji cewa jigon jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Bola Tinubu, ya ce ba zai taba kasance da hannu a cikin kowani irin barna da ta’addanci ba.

KU KARANTA KUMA: Da duminsa: Matasa sun kone gidan iyayen Gwamnan Legas, Sanwo-Olu

Tinubu na martani ne ga harin daren ranar Talata, 20 ga watan Oktoba, wanda aka gano jami’an tsaro suna bude wuta a kan masu zanga-zangar EndSARS a Lekki da ke Lagas.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng