An tsaurara matakan tsaro a Kaduna yayinda zanga-zanga ke yaduwa

An tsaurara matakan tsaro a Kaduna yayinda zanga-zanga ke yaduwa

- An jibge matakan tsaro a garin Kaduna da gidan gwamnatin jihar

- Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da zanga-zanga ke bazuwa a fadin kasar

- Ko a ranar Talata, 20 ga watan Oktoba, sai da masu zanga-zangar suka bukaci ganin Gwamna Nasir El-Rufai a gidan gwamnati

An tsaurara matakan tsaro a kewayen birnin Kaduna da gidan gwamnati a ranar Talata, 20 ga watan Oktoba yayinda zanga-zangar #SecureNorth ke kara yaduwa a fadin kasar, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Rahoton jaridar ya bayyana an gano motocin yan sanda jibge a kewaye da shataletalen gidan gwamnati tare da yan sanda masu kayan aiki da misalin karfe 10:00 na safe.

KU KARANTA KUMA: EndSARS: Kada ka yi amfani da karfin iko kan masu zanga-zanga - Atiku ga Buhari

An tsaurara matakan tsaro a Kaduna yayinda zanga-zanga ke yaduwa
An tsaurara matakan tsaro a Kaduna yayinda zanga-zanga ke yaduwa Hoto: @GuardianNigeria
Asali: UGC

Masu zanga-zangar sun je gidan gwamnati a ranar Litinin inda suka ce lallai sai sun ga Gwamna Nasir Ahmad El-Rufai.

A ranar Talata masu zanga-zanngar sun taru a majalisar dokokin jihar da misalin karfe 12:00 na rana tare da ganga da kayen kida suna rawa da ihun “A tsare arewa yanzu”, “A kawo karshen ta’addanci,”da kuma “A kawo karshen garkuwa da mutane.”

KU KARANTA KUMA: An yi arangama tsakanin ƴan sanda ta ɓata gari a Lagos, mutane 2 sun mutu

A wani labarin, Gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu ya yi maza ya kai ziyara ga wadanda aka buda wa wuta wajen zanga-zangar #EndSARS a Lekki.

Mista Babajide Sanwo-Olu ya yi magana a dandalin Twitter da kimanin karfe 4:00 na safe.

Gwamnan ya kira lamarin abin takaici da bakinciki, ya ce abin ya da auku ya fi karfin ikon gwamnati, ya yi alkawarin yin jawabi a yau da safe.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng