Bidiyon wani mai bayar da hannu a titi da masu zanga-zanga suka karrama saboda kwazonsa

Bidiyon wani mai bayar da hannu a titi da masu zanga-zanga suka karrama saboda kwazonsa

- A kwanan nan ne aka karrama wani dan sanda mai bayar da hannu a titi a yayinda yake bakin aiki

- A cewar rahotanni, wasu masu zanga-zanga a Calabar sun taru domin karrama shi saboda kwazonsa

- A wani bidiyo da aka wallafa, an gano inda masu zanga-zangar suka daga mutumin sama sannan suka ta yi masa liki da kudi

Wasu masu zanga-zangar a kawo karshen SARS a garin Calabar, sun karrama wani dan sanda mai bayar da hannu a titi, sun nuna masa so da kauna tare da tallafa masa.

A wani bidiyo da shafin @mediagist ta wallafa a Instagram, an nuno yadda matasan suka karrama mutumin tare da taya shi murna a yayinda yake bakin aikinsa.

A bisa ga wallafar, an bayyana mutumin mai suna Igri Nna Nkanu, a matsayin jajirtacce kuma mai kwazo a kan aikinsa.

KU KARANTA KUMA: Lawan ya dauki nauyin aurar da marayu da marasa gata su 100 a Yobe

Bidiyon wani mai bayar da hannu a titi da masu zanga-zanga suka karrama saboda kwazonsa
Bidiyon wani mai bayar da hannu a titi da masu zanga-zanga suka karrama saboda kwazonsa Hoto: @JC_Jokes
Asali: Twitter

Taron wanda ya gudana a ranar Juma’a, 16 ga watan Oktoba, ya nuno yadda mutane suka taru a kanshi, sannan suka daga shi sama a kan kokarin da yake yi kan aikinsa.

A cikin bidiyon, an gano wasu masu zanga-zanga suna masa liki da kudi.

Wani mai amfani da Twitter @JC_Jokes ya wallafa bidiyon inda ya rubuta:

“Masu zanga-zanga sun karrama mai bayar da hannu a titi mafi kwazo a Calabar. A koda yaushe za ku ganshi yana aikinsa da murmushi a fuskarsa a hanyar Mary Slessor. Har tara masa kudi suka yi. Yan Najeriya sun kasance mutane masu karamci duk da halin da ake ciki!”

KU KARANTA KUMA: Ambaliya: Buhari ya aika da tallafi Kaduna, Kano, Kebbi da wasu jihohi 9

A wani labari na daban, wata yar Najeriya ta je shafin soshiyal midiya domin murnar nasarar da ta samu bayan ta yi tattaki daga Lagas zuwa Abuja a kan babur.

Matashiyar mai suna Fehintoluwa Okegbenle ta wallafa wasu hotunanta da na sauran mutane da suka yi tafiyar a shafinta na Twitter.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng