Wata sabuwa: Ƴan daba sun tarwatsa masu zanga zanga a Kano

Wata sabuwa: Ƴan daba sun tarwatsa masu zanga zanga a Kano

- Wasu da ake zaton yan daba ne sun far ma masu zanga-zanga a jihar Kano

- Yan daban sun tarwatsa matasan wadanda suka fito don nuna damuwarsu a kan rashin tsaro a yankin arewacin kasar a daidai titin Kabuga

- Sun kuma yi masu sace-sacen wayoyi inda hakan ya sa suka hakura da gangamin

Rahotanni da muke samu a yanzu, ya nuna cewa wasu yan daba dauke da makamai sun tarwatsa zanga-zangar da wasu matasa ke gudanarwa a jihar Kano.

Matasa a jihar dai sun fito domin yin gangami a kan matsalar tsaro da ake fama da ita a arewacin Najeriya.

KU KARANTA KUMA: Tashin farashin masara, tumatur, dawa: Jihar Nigeria da ke fuskantar ƙarancin abinci

Wata sabuwa: Ƴan daba sun tarwatsa masu zanga zanga a Kano
Wata sabuwa: Ƴan daba sun tarwatsa masu zanga zanga a Kano Hoto: @bbchausa
Asali: Twitter

Sashin Hausa na BBC ta ruwaito cewa yan daban sun far wa masu zanga-zangar ne daidai titin kabuga da ke birnin tare da kwace-kwacen wayoyi.

Hakan ya tursasa wa masu zanga-zangar hakura da ci gaba da tattakin nasu.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Gwamna El-rufa’i ya sanya ranar buɗe makarantu a Kaduna

A wani lamari makamancin haka, wasu batagari, da ake kyautata zaton 'yan daba ne, dauke da makamai sun kai hari a kan wasu matasa da ke zanga-zanga a kan zaluncin da 'yan sandan rundunar SARS ke yi a fadin Najeriya.

'Yan daban, wadanda ke dauke da adduna, sun kai wa masu zanga-zangar farmaki a daidai Berger, bayan kusan sa'a daya da fara zanga-zangar.

Batagarin matasan sun ci mutuncin masu zanga-zangar har da masu wucewa, inda suka lalata ababen hawa da dama da ke wurin.

Rahotanni sun bayyana cewa 'yan dabar sun lalata akalla motoci 5 nan take, sannan sun ji wa masu zanga-zanga da dama munanan raunuka.

Wani matashi daga cikin wadanda aka ragargajewa mota ya ci kuka sharaf-sharaf da hawaye saboda bakin ciki.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng