Ta’addanci: Yan gudun hijira na iya komawa Baga domin akwai tsaro yanzu, gwamnatin Borno

Ta’addanci: Yan gudun hijira na iya komawa Baga domin akwai tsaro yanzu, gwamnatin Borno

- An kaddamar da cewar yan gudun hijira na iya komawa garin Baga da ke Borno

- Kwamishinan shari’a a jihar, Kaka-Shehu Lawan ne ya bayyana hakan

- Lawan a ranar Talata, 13 ga watan Oktoba, ya bayyana cewa sojojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro na ba garin kariya

Ana shirye-shiryen mayar da yan gudun hijira da ke Borno zuwa garin Baga, daya daga cikin wuraren da yan ta’addan Boko Haram suka kaddamar da hare-hare a baya-bayan nan.

Atoni janar kuma kwamishinan shari’a a jihar, Kaka-Shehu Lawan, a ranar Talata, 13 ga watan Oktoba, ya yi bayani kan dalilin da yasa gwamnati ta yanke wannan shawarar.

KU KARANTA KUMA: Abubuwa 5 da ya kamata mutum ya guji aikatawa a yayin zanga-zanga

Lawan, kamar yadda jaridar Premium Times ta ruwaito, ya yi ikirarin cewa garin Baga na da cikakken tsaro a yanzu da yan gudun hijira za su iya komawa.

Hakan ya biyo bayan hare-hare biyu da aka kai wa motocin Gwamna Babagana Zulum a garin.

Ta’addanci: Yan gudun hijira na iya komawa Baga domin akwai tsaro yanzu, gwamnatin Borno
Ta’addanci: Yan gudun hijira na iya komawa Baga domin akwai tsaro yanzu, gwamnatin Borno Hoto: @PremiumTimesng
Asali: Twitter

Kwamishinan wanda ke jagorantar kwamitin da ke kula da ragamar mayar da yan gudun hijiran, ya ce lallai hare-haren da aka kai wa gwamnan bai da nasaba da yanayin tsaron garin gaba daya.

KU KARANTA KUMA: EndSARS: Gwamnan Lagas ya gana da Buhari a Aso Rock

Harma Lawan ya ce shi da tawagarsa sun shafe tsawon kwanaki hudu a garin Baga a lokacin sake bude garin kuma basu fuskanci wani lamari na tashin hankali ba.

Ya jadadda cewa a yanzu garin cike yake da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin bayar da kariya.

Ya ce:

“Kwamitinmu ya shafe kwanaki hudu a garin kuma ina iya tabbatar maku da cewa akwai tsaro sosai a Baga kuma akwai tarin sojoji a wajen.

“A kwanaki hudu da muka kwashe a Baga, bamu samu wani barazana na tsaro ba. Mun fita mun yi yawo a garin don duba ayyukan da ya kamata ayi ba tare da fargaba ba.

"Bayan aikin rangadin mu kan koma masaukinmu da ke cikin garin mun kwana. Ba a samu lamari na harbi ba ko sau daya.

“Hatta lokacin da gwamnan ya zo, ya kwana a Baga kuma ba a samu tashin hankali ba.”

A wani labarin, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, a ranar Talata, 13 ga watan Oktoba, ya bukaci hukumar yan sanda da ta tura jami’an rundunar SARS da aka rushe zuwa jihar domin bayar da gudunmawa a yaki da yan ta’addan Boko Haram.

An dai soke sashin rundunar ta yan sanda sannan aka rarraba jami’ata zuwa wasu bangarorin biyo bayan zanga-zangar kawo karshen rundunar SARS da aka gudanar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng