Ta’addanci: Yan gudun hijira na iya komawa Baga domin akwai tsaro yanzu, gwamnatin Borno

Ta’addanci: Yan gudun hijira na iya komawa Baga domin akwai tsaro yanzu, gwamnatin Borno

- An kaddamar da cewar yan gudun hijira na iya komawa garin Baga da ke Borno

- Kwamishinan shari’a a jihar, Kaka-Shehu Lawan ne ya bayyana hakan

- Lawan a ranar Talata, 13 ga watan Oktoba, ya bayyana cewa sojojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro na ba garin kariya

Ana shirye-shiryen mayar da yan gudun hijira da ke Borno zuwa garin Baga, daya daga cikin wuraren da yan ta’addan Boko Haram suka kaddamar da hare-hare a baya-bayan nan.

Atoni janar kuma kwamishinan shari’a a jihar, Kaka-Shehu Lawan, a ranar Talata, 13 ga watan Oktoba, ya yi bayani kan dalilin da yasa gwamnati ta yanke wannan shawarar.

KU KARANTA KUMA: Abubuwa 5 da ya kamata mutum ya guji aikatawa a yayin zanga-zanga

Lawan, kamar yadda jaridar Premium Times ta ruwaito, ya yi ikirarin cewa garin Baga na da cikakken tsaro a yanzu da yan gudun hijira za su iya komawa.

Hakan ya biyo bayan hare-hare biyu da aka kai wa motocin Gwamna Babagana Zulum a garin.

Ta’addanci: Yan gudun hijira na iya komawa Baga domin akwai tsaro yanzu, gwamnatin Borno
Ta’addanci: Yan gudun hijira na iya komawa Baga domin akwai tsaro yanzu, gwamnatin Borno Hoto: @PremiumTimesng
Asali: Twitter

Kwamishinan wanda ke jagorantar kwamitin da ke kula da ragamar mayar da yan gudun hijiran, ya ce lallai hare-haren da aka kai wa gwamnan bai da nasaba da yanayin tsaron garin gaba daya.

KU KARANTA KUMA: EndSARS: Gwamnan Lagas ya gana da Buhari a Aso Rock

Harma Lawan ya ce shi da tawagarsa sun shafe tsawon kwanaki hudu a garin Baga a lokacin sake bude garin kuma basu fuskanci wani lamari na tashin hankali ba.

Ya jadadda cewa a yanzu garin cike yake da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin bayar da kariya.

Ya ce:

“Kwamitinmu ya shafe kwanaki hudu a garin kuma ina iya tabbatar maku da cewa akwai tsaro sosai a Baga kuma akwai tarin sojoji a wajen.

“A kwanaki hudu da muka kwashe a Baga, bamu samu wani barazana na tsaro ba. Mun fita mun yi yawo a garin don duba ayyukan da ya kamata ayi ba tare da fargaba ba.

"Bayan aikin rangadin mu kan koma masaukinmu da ke cikin garin mun kwana. Ba a samu lamari na harbi ba ko sau daya.

“Hatta lokacin da gwamnan ya zo, ya kwana a Baga kuma ba a samu tashin hankali ba.”

A wani labarin, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, a ranar Talata, 13 ga watan Oktoba, ya bukaci hukumar yan sanda da ta tura jami’an rundunar SARS da aka rushe zuwa jihar domin bayar da gudunmawa a yaki da yan ta’addan Boko Haram.

An dai soke sashin rundunar ta yan sanda sannan aka rarraba jami’ata zuwa wasu bangarorin biyo bayan zanga-zangar kawo karshen rundunar SARS da aka gudanar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel