Zulum ya goyi bayan SARS, yana so a dawo da jami’an rundunar jiharsa

Zulum ya goyi bayan SARS, yana so a dawo da jami’an rundunar jiharsa

- Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno ya bayyana matsayarsa kan rundunar SARS

- Zulum ya ce yana goyon bayan rundunar dari-bisa-dari

- Ya bukaci hukumar yan sanda ta dawo da rundunar wacce aka rushe jiharsa domin su yi yaki da ta'addanci

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, a ranar Talata, 13 ga watan Oktoba, ya bukaci hukumar yan sanda da ta tura jami’an rundunar SARS da aka rushe zuwa jihar domin bayar da gudunmawa a yaki da yan ta’addan Boko Haram.

An dai soke sashin rundunar ta yan sanda sannan aka rarraba jami’anta zuwa wasu bangarorin biyo bayan zanga-zangar kawo karshen rundunar SARS da aka gudanar a kasar.

Kasa da kwanaki biyu bayan soke rundunar yan sandan, an sake gudanar da gagarumin zanga-zanga kan ayyukanta a ranar Talata a fadin kasar.

KU KARANTA KUMA: Abubuwa 5 da ya kamata mutum ya guji aikatawa a yayin zanga-zanga

Zulum ya yi kiran ne a lokacin da wata tawaga karkashin jagorancin ministan cikin gida, Rauf Argebesola suka gana da shi a gidan gwamnati, Maiduguri, Daily Trust ta ruwaito.

Zulum ya goyi bayan SARS, yana so a dawo da jami’an rundunar jiharsa
Zulum ya goyi bayan SARS, yana so a dawo da jami’an rundunar jiharsa Hoto: @daily_trust
Asali: Twitter

Gwamnan ya ce jami’an rundunar da aka soke sun taka muhimmiyar rawar gani a ayyukan yaki da ta’addanci da karfinsu musamman a yaki da Boko Haram.

Ya ce: “Ba ma goyon bayan cin zarafi daga kowani jami’in tsaro, amma maganar gaskiya, a nan jihar Borno bai kamata a wofantar da kokarin jami’an SARS ba a yaki da suke da ta’addanci.

“Suna kokari matuka wajen magance matsalar tsaro a jihar Borno. Sun taimakawa kokarin rundunar sojin Najeriya sosai,” in ji Zulum.

KU KARANTA KUMA: EndSARS: Gwamnan Lagas ya gana da Buhari a Aso Rock

A baya mun ji cewa wasu kungiyoyin jama’a da na yan kasuwa a jihar Borno sun fito unguwa don yi zanga-zangar rashin jin dadi ruguza rundunar yan sandan SARS da gwamnatin Tarayya ta yi.

Masu zanga-zangar na so rundunar SARS ta ci gaba da ayyukanta a jihar Borno.

Shugaban gamayyar kungiyar a Borno, Ahmed Shehu, ya ce koda dai basa farin ciki da Abunda ke gudana a wasu sassan kasar, “jami’an SARS sun taimaka sosai wajen yaki da ta’addanci.”

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng