KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana

A yau Asabar, 10 ga watan Oktoban 2020, jama'ar jihar Ondo za su kada kuri'unsu domin zaben gwamna na 7 a cikin shekaru 44 da kafuwar jihar.

Legit.ng za ta dinga kawo muku rahoto dalla-dalla kai tsaye daga jihar Ondo.

A zaben yau, jam'iyyyun siyasa 17 wadanda suka hada da APC da PDP duk sun fitar da 'yan takararsu.

Masu ruwa da tsaki a jihar sun bayyana tsoronsu na yuwuwar rikici, ganin cewa akwai tarihin rikicin zabe da tashin-tashina a jihar.

An kammala jefa kuri'a a wasu rumfunan zabe, an fara kidaya

An kammala jefa kuri'a kuma an fara kidaya yanzu haka a rumfar zabe mai lamba 02, gunduma ta 4 a Idanre lGA (TheCable)

An kammala jefa kuri'a kuma an fara kidaya yanzu haka a rumfunan zabe da dama dake gunduma ta 06 a karamar hukumar Akoko Northwest

An kama masu sa ido kan zabe na bogi da ake zargin Jam'iyyar PDP suka yi wa aiki a Ondo

An cafke wasu masu sa ido kan zabe na bogi da ake zargin jam'iyyar PDP suke yi wa aiki a yankin Ijomu a Akure ta jihar Ondo.

Mai kada kuri'a ya yanke jiki ya fadi a layin zabe

Wani mai kada kuri'a a gunduma ta 10 da ke Oke-Otunba, rumfa ta 7 da ke MDS Ododigbo/Okedibo II, ya yanke jiki ya fadi a layin zabe.

An gano cewa mai kada kuri'ar yana fama da farfadiya.

Dan takaran gwamnan PDP, Eyitayo Jegede, ya kada kuri’ar

Mataimakin gwamnan jihar Ondo kuma dan takarar gwamna na ZLP, Ajayi ya kada kuri'arsa

Mataimakin gwamna kuma dan takarar gwamna karkashin jam'iyyar ZLP, Agboola Ajayi a rumfar zabensa ta Kiribo da ke karamar hukumar Ese Ondo a jihar Ondo.

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
Agboola Ajayi ya kada kuri'arsa. Hoto: @MobilePunch
Asali: Twitter

Tsirarun masu zabe sun fara kada kuri'a bayan ruwan sama ya tsagaita a Ondo

Masu zabe sun fara dawowa don cigaba da kara kuri'unsu bayan ruwan sama ya tsagaita a Ondo.

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
An cigaba da zabe bayan ruwan sama a Ondo. Hoto: @MobilePunch
Asali: Twitter

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
An cigaba da zabe bayan ruwan sama a Ondo. Hoto: @MobilePunch
Asali: Twitter

Wasu wakilan jam'iyyun siyasa sun fara sayan kuri'a a garin Illaje na jihar Ondo

Wasu wakilan jam'iyyun siyasa sun fara sayan kuri'a a garin Illaje

@CDDWestAfrica ce ta gano siyan kuri'un

@MatthewTPage ya ce irin wannan lamarin ya saba faruwa a garuruwan da ke da wuyan zuwa

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
Wakilan jam'iyya suna sayar kuri'un masu zabe a jihar Ondo. Hoto: @Legitngnews
Asali: Twitter

Dan majalisa Olubunmi ya isa rumfar zabensa da ke Akoko

Olubunmi Tunji-Ojo, shugaban kwamitin majalisar wakilai na NDDC, ya isa rumfar zabensa ta 13,, gunduma ta 3 da ke karamar hukumar Akoko ta arewa maso yamma a jihar.

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana. Hoto daga @Thecable
Asali: Twitter

Gwamna Rotimi Akeredolu ya kada kuri'ansa

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
Gwamna Akeredolu ya jefa kuri'ansa. Hoto: @MobilePunch
Asali: Twitter

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
Gwamna Akeredolu yana kada kuri'a. Hoto: @MobilePunch
Asali: Twitter

Gwamnan Akeredolu ya isa rumfar zabensa da ke Ijebu Owo tare da matarsa

Gwamnan jihar Ondo, kuma dan takara a karkashin jam'iyyar APC, Akeredolu Rotimi, ya isa rumfar zabensa tare da matarsa a Ijebu Owo.

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana. Hoto daga @Mobilepunch
Asali: Twitter

Jami'an tsaro a kan babura za su kai kayayyakin zabe rumfar zabe a Akure-Owo road a jihar Ondo

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
Jami'an tsaro kan babur za su kai kayan zabe rumfar zabe a Akure jihar Ondo. Hoto @MobilePunch
Asali: Twitter

Dan takarar PDP, Jegede tare da matarsa sun isa rumfar zabensu

Dan takarar gwamnan jihar Edo, karkashin jam'iyyar PDP, Eyitayo Jegede, ya isa rumfar zabensa mai lamba 9 a gunduma ta 2 da ke karamar hukumar Akure ta Kudu.

Ruwan sama ya tarwatsa masu kada kuri'a a karamar hukumar Akure ta arewa

Akwati na 7 a gunduma ta 2 ta karamar hukumar Akure ta arewa, jama'a sun fara kada kuri'a amma ruwa ya tarwatsasu inda suka bazama neman mafaka.

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana. Hoto daga @Premiumtimes
Asali: Twitter

Ma'aikacin wucin-gadi yana wayar wa da masu kada kuri'a kai

A Agba, akwati na 08, gunduma ta 4 da ke karamar hukumar Akoko ta kudu masu yamma, shugaban akwatin zaben yana wayar wa masu kada kuri'a kai kafin fara zaben.

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana. Hoto daga @Thecable
Asali: Twitter

Ma'aikatan zabe sun fara lika rijistar wadanda za su yi zabe

Ma'aikatan zabe sun fara isa rumfunan zabe inda suke lika rijistar wadanda za su yi zabe.

KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana
KAI TSAYE: Yadda zaben jihar Ondo yake gudana. Hoto daga @tvnewsng
Asali: Twitter

Online view pixel