Katsina: Buhunan hatsi su na yin sauki bayan shigowar amfanin gona

Katsina: Buhunan hatsi su na yin sauki bayan shigowar amfanin gona

- Rahotanni sun ce farashin kayan abinci sun fara sauka a kasuwanni

- A yankin Kaduna da Katsina, hatsi sun rage tsada a kwanakin nan

- Hakan na zuwa ne bayan an fara cire kayan amfanin noman damina

Rahotanni daga jaridar Katsina Post sun bayyana cewa kayan abinci sun fara rage kudi a halin yanzu.

Masu saida hatsi da dillalai sun tabbatar da cewa buhunan kayan gona su na rage kudi a wasu manyan kasuwannin hatsi da ake da su.

Ana zargin hakan bai rasa alaka da sababbin hatsin da su ka fara shigowa a sakamakon girbe kayan amfanin gona da manoma su ka fara yi.

‘Yan jaridar sun tabbatar da cewa abinci sun rage kudi a halin yanzu, bayan sun kai ziyara zuwa kasuwannin Babbar Ruga da ta ‘Yar kutungu.

KU KARANTA: Ba za a dade ana fama da tsadar kayan abinci ba - Hadimin Buhari

Ana yin cinikin hatsi a wadannan kasuwanni da ke cikin karamar hukumar Batagarawa da Katsina.

Jaridar ta bayyana cewa a kasuwar Babbar Ruga, buhun gero ya tashi ne a kan N14, 000, akasin N26, 000 da aka saida shi a makon da ya gabata.

Haka zalika buhun masara ya rage kudi a yanzu, daga N23, 000 an koma saida buhu a kan N20, 000.

A wadannan kasuwanni, ana saida sabuwar masara wacce ta shigo gari a kimanin N14, 000.

Katsina: Buhunan hatsi su na yin sauki bayan shigowar amfanin gona
Kayan abinci Hoto: Legit
Asali: Original

KU KARANTA: Abin da ya jawo mana tsadar abinci - Buhari

Mudun gero ya koma N400 maimakon N500 da aka rika saida shi a kasuwar ‘Yan kutungu kwanakin baya, an samu raguwar kusan 30% a farashi.

A kasuwar Saminaka ma dai hatsi sun rage tsada, sabuwar masara ta karye. Haka zalika farashin babban buhun shinkafa ya fadi war-was a makon jiya.

A kwanan baya aka ji Hadimin shugaban kasa, Garba Shehu ya na cewa farashin hatsi ya na sauka a Najeriya bayan mugun tsadar da su ka yi a watan nan.

Shehu ya yi wannan jawabin ne a dalilin kukan da ‘yan kasa su ke yi na tsadar halin rayuwa.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel