Osinbajo: Mataimakin Shugaban kasa ya bankado badakala a yarjejeniyar P & ID

Osinbajo: Mataimakin Shugaban kasa ya bankado badakala a yarjejeniyar P & ID

Wani Alkalin Birtaniya, ya ce maza-mazan da Farfesa Yemi Osinbajo ya yi, ya taimaka wajen gano cuwa-cuwar da aka nemi a tafka a yarjejeniyar P & ID.

Alkali mai shari’a Ross Cranston a babban kotun Birtaniya, ya ce mataimakin shugaban kasar Najeriya ya bi diddiki, ya gano damfarar da aka shimfida a wannan yarjejeniya.

Sir Ross Cranston ya ce jawabin da Farfesa Yemi Osinbajo ya fitar mai taken “fraud on the nation” a 2018 a kan damfarar da ake neman yi wa Najeriya, ya yi tasiri sosai.

Jaridar Pulse ta fitar da wannan dogon rahoto a ranar 5 ga watan Satumba, 2020.

Alkalin ya ce Yemi Osinbajo ya fara bibiyar wannan yarjejeniya ne tun a shekarar 2017, bayan Ministan shari’a, Abubakar Malami SAN, ya sanar da shi halin da ake ciki.

KU KARANTA: Buhari ya sake fadawa Ministocinsa su nemi COS idan su na son ganinsa

Babban Alkalin ya ce: "Bayan wata zama da aka yi a ranar 13 ga watan Maris, 2017, Malami ya rubutawa mataimakin shugaban kasa takarda, a lokacin ya na shugaban rikon-kwarya.”

Ministan shari’an Najeriyar ya yi wa Farfesa Osinbajo bayanin halaye biyar da Najeriya za ta iya samun kanta, da kuma shawarwarin abin da ya kamata ayi a duk yadda ta kama.

Malami SAN ya fadawa Osinbajo cewa abin yi shi ne ayi sulhu da P & ID a wajen kotu, ko kuma a binciki ainihin yarjejeniyar da kamfanin ya shiga da Najeriya domin gano tuntube.

Tsakanin Afrilu da Mayun 2017, Mai girma Osinbajo ya yi na’am da zama ayi sulhu da kamfanin P & ID, a karshe shirin yin sulhu a wajen kotu da wannan kamfani bai yiwu ba.

KU KARANTA: Jawabin Shugaba Akufo-Addo na zama Shugaban ECOWAS

Kokarin da Osinbajo ya yi ya zarce na ikon da ya ke da shi a matsayin mukaddashin shugaban kasa, ya karbi maganar Ministan shari’a, kuma ya rubutawa Buhari takarda.

Ministan shari’a da na mai a lokacin sun nemi ayi sulhu, amma Osinbajo ya dauki lokaci na musamman, ya duba yarjejeniyar da kyau, ya ce ana neman a cuci gwamnatin tarayya.

A karshe wannan ya yi sanadiyya aka koma kotu, har ta kai Najeriya ta fara samun nasara a shari’ar da aka yanke na cewa gwamnatin kasar za ta biya P & ID tarar Dala biliyan 9.6.

Ku na da labari cewa an shiga yarjejeniya da P & ID ne a lokacin da Marigayi Ummaru ‘Yar’adua bai da lafiya, sa'ilin da Goodluck Jonathan ya ke mukaddashin shugaban kasa.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel