Rundunar soji ta kashe yan ta’adda 9, sun ceto mutum 7 a Gwoza

Rundunar soji ta kashe yan ta’adda 9, sun ceto mutum 7 a Gwoza

- Dakarun Operation Lafiya Dole da ke yaki da ta’addanci a yankin arewa maso gabas sun kashe yan ta’adda tara a yayin wata kakkaba a karamar hukumar Gwoza da ke Borno

- Rundunar Bataliya 192 da taimakon rundunar sama ne suka kai hari kan yan ta'addan a garin Hamdaga Makaranta da ke Gwoza

- Dakarun sun kakkabe gine-gine tara da gonakin Boko Haram da ISWAP a yankin

Rundunar sojin Najeriya a ranar Litinin ta ce dakarunta na Operation Lafiya Dole da ke yaki da ta’addanci a yankin arewa maso gabas sun kashe yan ta’adda tara a yayin wata kakkaba a karamar hukumar Gwoza da ke jihar Borno.

Jagoran labarai na ayyukan rundunar tsaro, Manjo Janar John Enenche ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa.

Ya ce bisa bayanai abun dogaro da suka samu kan ayyukan yan ta’addan a garin Hamdaga Makaranta da ke Gwoza, rundunar Bataliya 192 da taimakon rundunar sama a ranar 6 ga watan Satumba 2020, sun kai mamaya wajen.

KU KARANTA KUMA: Yan bindiga sun halaka wani hazikin sojan sama a Kaduna (hoto)

Rundunar soji ta kashe yan ta’adda 9, sun ceto mutum 7 a Gwoza
Rundunar soji ta kashe yan ta’adda 9, sun ceto mutum 7 a Gwoza
Source: UGC

Ya ce dakarun sojin sun yi nasara kan yan ta’addan inda suka kashe mutum biyar yayinda sauran suka tsere da raunukan bindiga.

Rundunar sun kakkabe gine-gine tara da gonakin Boko Haram da ISWAP a yankin.

Ya um ace rundunar sun cceto mutum bakwai da aka yi garkuwa da su wadanda suka hada da mata biyu da yara biyar.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Gidaje, shaguna sun kone kurmus yayinda motar tanka ta kama da wuta a jihar Neja

A wani labari makamancin wannan, rundunar sojoji na Operation Whirl Stroke a jihohin Benue da Nasarawa sun kashe yan bindiga biyar yayinda suka kama wasu takwas.

Manjo Janar John Enenche, ya ce an kashe yan bindiga hudu a yayin wani mamaya da aka kai mabuyarsu a Tse Agi, karamar hukumar Gwer ta yamma a jihar Benue.

Ya kuma bayyana cewa an kashe daya daga cikin yan bindigan a lokacin da dakarun suka kai farmaki sansaninsu da ke iyakar Benue-Nasarawa.

Eneche wanda ya bayyana cewa an samo alburusai da dama a yayin arangaman, ya yaba ma jama’a a kan bayar da muhimman bayanai na kwararru wanda ya sa aka cimma nasara.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng