Wani sojan Najeriya ya wallafa hotunan abokan aikinsa da Boko Haram suka kashe a Maiduguri

Wani sojan Najeriya ya wallafa hotunan abokan aikinsa da Boko Haram suka kashe a Maiduguri

Wani sojan Najeriya mai suna Emmanuel, a ranar Asabar, 5 ga watan Satumba, ya nuna alhini a kan mutuwar wasu abokan aikinsa da suka mutu a filin daga.

Emmanuel ya wallafa hotunan abokan nasa wadanda ya ce sun mutu a yayin arangama da ‘yan ta’addan Boko Haram a Maiduguri, babbar birnin jihar Borno, shafin Linda Ikeji ta ruwaito.

Ku tuna cewa akalla sojoji ashirin aka kashe sannan wasu da dama suka bata bayan hare-hare mabanbanta da kungiyar ISWAP wacce ta balle daga Boko Haram suka kai Borno a makon da ya gabata.

A cewar Emmanuel, sojojin sun “mutu a filin daga yayin arangama da mayakan Boko Haram a Maiduguri.”

Ga hotunan sojojin a kasa:

Wani sojan Najeriya ya wallafa hotunan abokan aikinsa da Boko Haram suka kashe a Maiduguri
Wani sojan Najeriya ya wallafa hotunan abokan aikinsa da Boko Haram suka kashe a Maiduguri
Source: UGC

Wani sojan Najeriya ya wallafa hotunan abokan aikinsa da Boko Haram suka kashe a Maiduguri
Wani sojan Najeriya ya wallafa hotunan abokan aikinsa da Boko Haram suka kashe a Maiduguri
Source: UGC

Wani sojan Najeriya ya wallafa hotunan abokan aikinsa da Boko Haram suka kashe a Maiduguri
Wani sojan Najeriya ya wallafa hotunan abokan aikinsa da Boko Haram suka kashe a Maiduguri
Source: UGC

KU KARANTA KUMA: 'Duk lauya Musulmi da ya ce zai kare wanda ya zagi Annabi Muhammadu (SAW) ya kafurta' - Malami

A baya mun kawo maku cewa an yi artabu a tsakanin sojojin Najeriya da mayakan kungiyar ISWAP a jihar Borno.

Kungiyar ta ISWAP ta yi ikirarin cewa mayakanta sun kashe sojojin Najeriya akalla guda 20 a hare-hare biyu da suka kai kan sojojin a jihar Borno, sashin Hausa na BBC ya ruwaito.

An tattaro cewa ‘yan ta’addan sun kai hari wani sansanin soji da ke Magumeri cikin motoci da aka girke manyan bindigogi a kansu.

Garin Magumeri na a tsawon kimanin kilomita hamsin daga Maiduguri, babban birnin Jihar ta Borno.

A cikin wata sanarwa, kungiyar ISWAP ta yi ikirarin cewa mayakanta sun kashe sojoji goma da kuma kwace makamai da motocin soji a yayin arangama da suka yi.

Kungiyar ta kuma yi ikirarin cewa ta kashe wasu karin sojoji 10 a wani kwanton-bauna kan ayarin sojojin a kusa da kauyen Kuros-Kauwa da ke yankin Baga.

An tattaro cewa dukkanin lamuran biyu sun faru ne a ranar Talata da ta gabata.

Sai dai kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito cewa majiyoyinsa sun tabbatar masa da cewa sojoji tara mayakan suka kashe a Magumeri.

Hakazalika rundunar sojin ta yi ikirarin kashe mayakan kungiyar a wani hari ta sama da dakarunta suka kai da jiragen yaki kan sansanin yan ta'addan a kauyen Kaza, kusa da Gulumba-Gana a yankin Bama cikin jihar ta Borno.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng