Abin alfaharinmu: Harshen Hausa ya zamo yare mafi saurin yaduwa a duniya

Abin alfaharinmu: Harshen Hausa ya zamo yare mafi saurin yaduwa a duniya

- Harshen Hausa ya kasance yare na biyu da aka fi yi kuma yana yaduwa cikin sauri

- Shugaban kungiyar Hausawa na Afrika, Dr Abdulkadir Labbaran Koguna, ya yi ikirarin cewa ana amfani da yaren Hausa a fadin duniya

- A cewarsa, majalisar dinkin duniya ta san da zaman yaren a matsayin na 11 cikin yaruka 70,250 na duniya

An bayyana harshen Hausa a matsayin daya daga cikin yaruka mafi saurin yaduwa kamar yadda ake amfani da ita a yankunan duniya da dama.

Da yake magana a kan shaharar yaren, shugaban kungiyar al’umman Hausawa na duniya, Dr Abdulkadir Labbaran Koguna, ya yi ikirarin cewa ana amfani da yaren a fadin duniya gaba daya.

Koguna ya yi wannan ikirari ne a wajen bikin ranar Hausa ta duniya na 2020 wanda aka gudanar a karamar hukumar Rano da ke jihar Kano.

Abin alfaharinmu: Harshen Hausa ya zamo yare mafi saurin yaduwa a duniya
Abin alfaharinmu: Harshen Hausa ya zamo yare mafi saurin yaduwa a duniya Hoto: Connect Nigeria
Asali: UGC

A cewar Koguna, wani sashi a majalisar dinkin duniya ya san da zaman harshen Hausa sannan ya sanya ta a matsayin na 11 cikin yaruka 70,250 na duniya, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Koguna ya ce: “Baya ga wannan, masarautar Saudiyya ma ta san da zaman yaren domin yana a cikin yaruka goma da aka fassara hudubar ranar Arafat na wannan shekarar.”

Har ila yau daga cikin wadanda suka yi magana a taron harda Farfesa Abdulqadir Dangambo, wanda ya bukaci gwamnati da ta bunkasa yaren ta hanyar amfani dashi a matsayin yare na daya musamman a arewa.

A halin da ake ciki, akwai wasu abubuwan ban sha’awa game da kabilar Hausa. Kabilar ce mafi girma a nahiyar Afrika da mutane miliyan 78.

KU KARANTA KUMA: Halima Abubakar: A yanke mazakutar wanda aka kama da laifin fyade

Harshen Hausa ne yare na biyu da aka fi amfani dashi a gida tare da kimanin mutum miliyan 120 da ke yinta.

Ana iya samun masu amfani da yaren a Najeriya, Nijar, Chadi, Benin, Kamaru, Togo, Jumhuriyar Afrika ta tsakiya, Ghana, Sudan, Eritrea, Equatorial Guinea, Gabon, Senegal, da Gambia.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel