Abin alfaharinmu: Harshen Hausa ya zamo yare mafi saurin yaduwa a duniya

Abin alfaharinmu: Harshen Hausa ya zamo yare mafi saurin yaduwa a duniya

- Harshen Hausa ya kasance yare na biyu da aka fi yi kuma yana yaduwa cikin sauri

- Shugaban kungiyar Hausawa na Afrika, Dr Abdulkadir Labbaran Koguna, ya yi ikirarin cewa ana amfani da yaren Hausa a fadin duniya

- A cewarsa, majalisar dinkin duniya ta san da zaman yaren a matsayin na 11 cikin yaruka 70,250 na duniya

An bayyana harshen Hausa a matsayin daya daga cikin yaruka mafi saurin yaduwa kamar yadda ake amfani da ita a yankunan duniya da dama.

Da yake magana a kan shaharar yaren, shugaban kungiyar al’umman Hausawa na duniya, Dr Abdulkadir Labbaran Koguna, ya yi ikirarin cewa ana amfani da yaren a fadin duniya gaba daya.

Koguna ya yi wannan ikirari ne a wajen bikin ranar Hausa ta duniya na 2020 wanda aka gudanar a karamar hukumar Rano da ke jihar Kano.

Abin alfaharinmu: Harshen Hausa ya zamo yare mafi saurin yaduwa a duniya
Abin alfaharinmu: Harshen Hausa ya zamo yare mafi saurin yaduwa a duniya Hoto: Connect Nigeria
Asali: UGC

A cewar Koguna, wani sashi a majalisar dinkin duniya ya san da zaman harshen Hausa sannan ya sanya ta a matsayin na 11 cikin yaruka 70,250 na duniya, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Koguna ya ce: “Baya ga wannan, masarautar Saudiyya ma ta san da zaman yaren domin yana a cikin yaruka goma da aka fassara hudubar ranar Arafat na wannan shekarar.”

Har ila yau daga cikin wadanda suka yi magana a taron harda Farfesa Abdulqadir Dangambo, wanda ya bukaci gwamnati da ta bunkasa yaren ta hanyar amfani dashi a matsayin yare na daya musamman a arewa.

A halin da ake ciki, akwai wasu abubuwan ban sha’awa game da kabilar Hausa. Kabilar ce mafi girma a nahiyar Afrika da mutane miliyan 78.

KU KARANTA KUMA: Halima Abubakar: A yanke mazakutar wanda aka kama da laifin fyade

Harshen Hausa ne yare na biyu da aka fi amfani dashi a gida tare da kimanin mutum miliyan 120 da ke yinta.

Ana iya samun masu amfani da yaren a Najeriya, Nijar, Chadi, Benin, Kamaru, Togo, Jumhuriyar Afrika ta tsakiya, Ghana, Sudan, Eritrea, Equatorial Guinea, Gabon, Senegal, da Gambia.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng