Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a manyan hukumomi tara

Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a manyan hukumomi tara

- Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a ma’aikatar labarai da al’adu

- An nada shugabanni tara na hukumomi da dama a ma’aikatar, ciki harda kamfanin dillancin labaran Najeriya

- Nadin zai fara aiki daga ranar Talata, 1 ga watan Satumba, 2020

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin manyan shugabanni na hukumomi tara a karkashin ma’aikatar labarai da al’adu ta tarayya.

A wata sanarwa da aka wallafa a shafin twitter na fadar shugaban kasar Najeriya, t ace wasikar amincewa da nade-naden ya isa ga ministan labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed, ta hannun Farfesa Ibrahim Gambari, shugaban ma’aikatan shugaban kasa a ranar Talata, 25 ga watan Agusta.

Legit.ng ta tattaro cewa nade-naden za su fara aiki daga ranar Talata, 1 ga watan Satumba, 2020.

Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a manyan hukumomi tara
Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a manyan hukumomi tara Hoto: The Cable
Asali: UGC

KU KARANTA KUMA: Buhari ya koka a kan yadda shari'ar manyan laifuka ke tafiyar 'Hawainiya'

Ga jerin sabbin nade-naden a kasa:

Mista Buki Ponle – Manajan Daraktan kamfanin dillancin labaran Najeriya

Mista Nura Sani Kangiwa – Darakta Janar na cibiyar bakunci da yawon bude ido

Mista Francis Ndubuisi Nwosu – Babban sakatare, kungiyar labarai ta Najeriya

Mista Ebeten William Ivara, Darakta Janar, hukumar zane-zane ta kasa

Mista Olalekan Fadolapo – Shugaban kungiyar tallace-tallace na Najeriya

Farfesa Sunday Enessi Ododo – Janar Manaja hukumar wasan kwaikwayo na kasa

Mista Ado Mohammed Yahuza – shugaban cibiyar al’adu ta kasa

Farfesa Aba Isa Tijjani – Darakta Janar na gidan tarihi da ajiya na kasa

Misis Oluwabunmi Ayobami Amao – Darakta anar na cibiyar kayan al’adu na bakar fata da Afrika

KU KAARANTA KUMA: Buhari ya amince da yi wa attajiran 'yan Najeriya karin kudin wutar lantarki

A gefe guda, mun ji cewa shugaba Muhammadu Buhari ya rantsar da sakatarorin dindindin guda goma sha biyu kafin a fara taron Majalisar Zartarwa ta Kasa karo na 13 da aka gudanar ta hanyar amfani da fasahar intanet a Abuja.

Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya samu hallartar taron rantsarwar da aka yi a dakin taron majalisar da ke fadar shugaban kasa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel