Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a manyan hukumomi tara

Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a manyan hukumomi tara

- Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a ma’aikatar labarai da al’adu

- An nada shugabanni tara na hukumomi da dama a ma’aikatar, ciki harda kamfanin dillancin labaran Najeriya

- Nadin zai fara aiki daga ranar Talata, 1 ga watan Satumba, 2020

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin manyan shugabanni na hukumomi tara a karkashin ma’aikatar labarai da al’adu ta tarayya.

A wata sanarwa da aka wallafa a shafin twitter na fadar shugaban kasar Najeriya, t ace wasikar amincewa da nade-naden ya isa ga ministan labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed, ta hannun Farfesa Ibrahim Gambari, shugaban ma’aikatan shugaban kasa a ranar Talata, 25 ga watan Agusta.

Legit.ng ta tattaro cewa nade-naden za su fara aiki daga ranar Talata, 1 ga watan Satumba, 2020.

Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a manyan hukumomi tara
Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya yi sabbin nade-nade a manyan hukumomi tara Hoto: The Cable
Asali: UGC

KU KARANTA KUMA: Buhari ya koka a kan yadda shari'ar manyan laifuka ke tafiyar 'Hawainiya'

Ga jerin sabbin nade-naden a kasa:

Mista Buki Ponle – Manajan Daraktan kamfanin dillancin labaran Najeriya

Mista Nura Sani Kangiwa – Darakta Janar na cibiyar bakunci da yawon bude ido

Mista Francis Ndubuisi Nwosu – Babban sakatare, kungiyar labarai ta Najeriya

Mista Ebeten William Ivara, Darakta Janar, hukumar zane-zane ta kasa

Mista Olalekan Fadolapo – Shugaban kungiyar tallace-tallace na Najeriya

Farfesa Sunday Enessi Ododo – Janar Manaja hukumar wasan kwaikwayo na kasa

Mista Ado Mohammed Yahuza – shugaban cibiyar al’adu ta kasa

Farfesa Aba Isa Tijjani – Darakta Janar na gidan tarihi da ajiya na kasa

Misis Oluwabunmi Ayobami Amao – Darakta anar na cibiyar kayan al’adu na bakar fata da Afrika

KU KAARANTA KUMA: Buhari ya amince da yi wa attajiran 'yan Najeriya karin kudin wutar lantarki

A gefe guda, mun ji cewa shugaba Muhammadu Buhari ya rantsar da sakatarorin dindindin guda goma sha biyu kafin a fara taron Majalisar Zartarwa ta Kasa karo na 13 da aka gudanar ta hanyar amfani da fasahar intanet a Abuja.

Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya samu hallartar taron rantsarwar da aka yi a dakin taron majalisar da ke fadar shugaban kasa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng