Boko Haram ta halaka farar hula 223 da jami'an tsaro 89 a cikin wata 7

Boko Haram ta halaka farar hula 223 da jami'an tsaro 89 a cikin wata 7

Kungiyar ta'addanci ta Boko Haram ta kashe farar hula 223, sojoji 82 da 'yan sanda bakwai a cikin watanni bakwai, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Lamarin, wanda ya auku tsakanin 2 ga watan Janairu zuwa 2 ga watan Augusta na wannan shekarar, ya faru ne a wurare daban-daban na jihohin Borno, Yobe da Adamawa.

Binciken ya nuna cewa, farar hula 21 da sojoji 13 sun jigata a cikin wannan lokacin.

Kusan makonni biyu da suka gabata, 'yan bindiga sun kai wa Gwamna Babagana Zulum hari a jihar Borno.

Lalacewar tsari a yankin arewa maso gabas ta sanya gwamnonin yankin suka zanta da shugaban kasa a jiya.

A taron, sun jaddada cewa 'yan ta'addan suna sake samun mambobi kuma akwai bukatar a yi wani abu don 'yan gudun hijira su koma gidajensu da gonakinsu.

A bangaren shugaban kasar, ya ce an samu nasarori masu tarin yawa a fannin tsaro amma dole ne shugabannin tsaro su kara kokari wurin tsaron kasar nan.

Boko Haram ta halaka farar hula 223 da jami'an tsaro 89 a cikin wata 7
Boko Haram ta halaka farar hula 223 da jami'an tsaro 89 a cikin wata 7 Hoto: Daily Post
Asali: UGC

A ranar 3 ga watan Janairun, an kashe farar hula uku a kauyen Bila-Ambokdar da ke karamar hukumar Chibok ta jihar Borno, sojoji hudu da wasu 11 sun jigata a Jakana a ranar 4 ga watan Janairu a Borno.

'Yan sanda biyU sun samu miyagun raunika a ranar 6 ga watan Janairu a kan babbar hanyar Maiduguri zuwa Damaturu yayin da aka kashe wasu uku a wannan ranar a kauyen Kundori da ke Konduga a Borno.

A ranar 7 ga watan Janairu, an kashe farar hula 30 yayin da wasu 35 suka samu raunika a Gamboru da ke karamar hukumar Gamboru Ngala a Borno.

Sojoji takwas da farar hula takwas aka kashe a ranar 7 ga watan Janairu a karamar hukumar Monguno.

A ranar 10 ga wata, 'yan ta'adda sun kashe farar hula uku a kan babbar hanyar Maiduguri zuwa Damaturu a karamar hukumar Konduga ta jihar Borno.

A ranar 17 ga watan Janairu, sojoji biyar sub rasa rayukansu yayin da 'yan ta'adda hudu suka rasu a karamar hukumar Bama ta jihar Borno.

A ranar 18 ga watan Janairu, sojoji hudu sun mutu a kan titin Bama zuwa Gwoza a karamar hukumar Gamboru-Ngala yayin da sojoji 8 suka rasu a ranar 21 ga watan Janairu a Mainok.

An kashe fararen hula 23 a kauyen Lura da ke karamar hukumar Dikwa a ranar 23 ga watan Janairu yayin da wasu hudu suka mutu washegari a Muna Galti da ke karamar hukumar Jere.

A masallacin Bulabulin da ke Gwoza, farar hula uku sun rasu yayin da 13 suka jigata a ranar 25 ga watan Janairu.

Farar hula uku suna rasu a kan babbar hanyar Damaturu zuwa Maiduguri yayin da biyu suka jigata, sai sojoji biyi da aka kashe a ranar 21 ga watan Fabrairu.

Sojoji uku sun rasu, wasu hudu sun jigata a ranar 4 ga watan Maris a Damboa. 'Yan sanda bakwai da farar hula daya sun rasu a garin Dapchi a ranar 5 ga watan Maris.

A ranar 21 ga watan Maris, sojoji 47 suka rasa rayukansu a kauyen Gorgi da ke Borno yayin da farar hula uku suka rasa ransu, wasu ukun suka jigata.

KU KARANTA KUMA: Ajali: Sauran sa'o'i kadan aurensa, ango ya yi mummunan hatsari

Farar hula bakwai sun rasu a ranar 13 ga watan Afirilu a kan titin Auno- Maiduguri-Damaturu, yayin da wani daya ya mutu a ranar 18 ga watan Afirilu a Buni Gari.

Farar hula 35 sun mutu a Usmanati Goni a ranar 13. Ga watan Yuni a Nganzai a Borno, yayin da farar hula 16 da sojoji tara suka rasu a babbar hanyar Damboa zuwa Maiduguri.

An kashe farar hula biyar a Moduri, Kalewa da Ngurori a ranar 21 ga watan Yuni a Magumeri da ke Borno, farar hula biyun mutu a Damasak a ranar 4 ga watan Yuli.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng