Mazauna Katsina sun sake gudanar da zanga-zanga kan hauhawan rashin tsaro

Mazauna Katsina sun sake gudanar da zanga-zanga kan hauhawan rashin tsaro

Fusatattun matasa a safiyar yau Alhamis, 6 ga watan Agusta sun toshe babban hanyar Kankara-Katsina, inda suka gudanar da zanga-zanga a kan hare-haren da ‘yan bindiga ke kai wa garuruwansu.

Mutanen sun yi amfani da manyan reshen bishiyoyi wajen kewaye hanyar kauyen Marken Dogon Ruwa a karamar hukumar Dutsima, inda suka dunga komar da masu motoci daga bangarori biyu na hanyar.

A yanzu haka daruruwan masu motoci da masu tafiya suna nan sun yi cirko-cirko a hanyar.

‘Yan fashi sun kai mamaya kauyukan Sanawa, Bera, Turare da Dogon Ruwa da ke karamar hukumar Dutsinma a daren ranar Laraba.

Mazauna Katsina sun sake gudanar da zanga-zanga kan hauhawan rashin tsaro
Mazauna Katsina sun sake gudanar da zanga-zanga kan hauhawan rashin tsaro Hoto: Daily Trust
Asali: UGC

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wata tawagar ‘yan sanda daga rundunar tsaron ta isa wajen, inda take kokarin tausar mutanen domin a bude hanyar.

Wannan shine karo na biyar da mazauna Katsina ke zanga-zanga kan rashin tsaro a jihar cikin watanni biyu da suka gabata.

An gudanar da zanga-zanga a garin Daddara da ke karamar hukumar Jibia, Yantumaki da ke karamar hukumar Danmusa da kuma Yankara da ke karamar hukumar Faskari.

KU KARANTA KUMA: Kada ku raba kan ahlinmu – Iyalan Obaseki sun karyata goyon bayan Ize-Iyamu

A baya mun ji cewa Gwamna Aminu Bello Masari na jihar Katsina ya gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadarsa da ke Abuja a ranar Laraba.

Masari ya ce ba za a bari kallubalen tsaro da ake fama da ita a jihohin Arewa maso Yamma da Arewa maso tsakiya ya tabarbare kamar matsayin da Boko Haram ya kai a Arewa maso Gabas.

Masari ya yi wannan jawabin ne yayin da ya ke amsa tambayar manema labarai a gidan gwamnatin bayan kammala taro da Shugaba Muhammadu Buhari a Abuja.

Ya ce a halin yanzu ana daukan dukkan matakan da suka dace domin kawo karshen hare haren yan bindiga da wasu laifukan a yankin na Arewa maso Yammacin kasar.

Gwamnan ya ce za a samu amfanin gona mai kyau a bana duk da cewa yan bindiga da wasu bata gari sun adabi manoma a kimanin kananan hukumomi tara a jihar ta Katsina.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng