DSS sun kama matasan da su ka fara zanga - zangar juyin hali a kudancin Najeriya

DSS sun kama matasan da su ka fara zanga - zangar juyin hali a kudancin Najeriya

Da safiyar yau, Laraba, ne jami'an hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) suka kama Olawale Bakare da wasu sauran mutane shida da ke sanye da huluna ruwan dorawa a yayin da su ka fito gudanar da zanga-zangar juyin juya hali.

Jami'an DSS sun kama matasan ne a yankin Olaiya da ke Osogbo, babban birnin jihar Osun.

Matasan a karkashin jagorancin Bakare sun yi tattaki zuwa ofishin 'yan jarida domin gabatar da jawabi a kan zanga-zangar da su ka fara.

A yayin da matasan su ke jira a gaban ofishin 'yan jaridar domin a yi mu su iso, sai wasu 'yan sanda su ka tunkarosu tare da fara tattaunawa dasu.

A yayin da su ke tattaunawa ne sai ga wasu jami'an tsaron na hukumar DSS sun dira a wurin tare da yin awon gaba da matasan.

DSS sun kama matasan da su ka fara zanga - zangar juyin hali a kudancin Najeriya
'Yan sanda yayin kokarin tarwatsa ma su zanga - zangar juyin hali
Asali: Facebook

Kazalika, jami'an rundunar 'yan sanda sun tarwatsa matasan da su ka fito zanga-zangar juyin juya hali da safiyar ranar Laraba a yankin Ikeja.

Jami'an rundunar 'yan sanda sun katse zanga - zangar da matasan su ka fara da misalin karfe 10:00 na safe.

DUBA WANNAN: El-Rufa'i ya mayarwa da sarakunan kudancin Kaduna martani a kan zargin kwace kasa

'Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa matasan.

Sai dai, wasu daga cikin matasan sun tirje, inda suka kwanta a kasa tare da rike takardun da su ke dauke dasu.

Hakan ya tilasta jami'an tsaro yin harbin iska domin tarwatsa ma su zanga-zangar.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa jami'an 'yan sanda sun kama matasa 60 daga cikin matasan da su ka fito zanga-zangar juyin juya hali a Abuja.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng