El-Rufa'i ya mayarwa da sarakunan kudancin Kaduna martani a kan zargin kwace kasa

El-Rufa'i ya mayarwa da sarakunan kudancin Kaduna martani a kan zargin kwace kasa

Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa'i, ya kalubalanci ma su rike da sarautar gargajiya a kudancin jihar a kan su nuna wani wuri da aka kwace a yankunansu tare da mikawa wasu mutane ko kungiyoyi ba bisa ka'ida ba.

Kazalika, El-Rufa'i ya kalubalanci sarakunan su bawa hukumomi da jami'an tsaro goyon baya a kokarinsu na tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a kudancin jihar Kaduna.

Ya zaburar dasu a kan su zama ma su adalci ga duk jama'ar da ke zaune a karkashin masarautunsu.

El-Rufa'i ya yi wadannan furuci ne a matsayin martani a kan zargin cewa wasu mutane sun kwace wasu sassan kudancin jihar Kaduna mai fama da yawaitar hare - hare a 'yan kwanakin baya bayan nan.

El-Rufa'i ya mayarwa da sarakunan kudancin Kaduna martani a kan zargin kwace kasa
El-Rufa'i
Asali: Depositphotos

Gwamnan ya fadi hakan ne ranar Talata yayin ganawarsa da majalisar sarakunan jihar, inda ya bayyana cewa gwamnatinsa ta dauki duk mazaunin wani yanki a matsayin dan jiha kamar yadda kundin mulki ya amince.

DUBA WANNAN: Magance matsalar tsaro: Buhari ya bada umurnin yin garambawul a rundunonin tsaro

Ya jaddada cewa yada labaran karya a kan gaskiyar halin da kudancin Kaduna ke ciki ba zai kashe gwuiwar gwamnatinsa a kokarinta na kawo karshen rikicin da aka shafe kusan shekara 40 ana fama da shi.

El-Rufa'i ya bayyana bakin cikinsa a kan yadda ake yada labarin karya a kan kwace gonaki da filayen jama'ar kudancn Kaduna.

Ya ce an fara amfani da wannan labarin karya a lokacin da rikici ya taba barkewa a yankin a shekarar 2016/2017.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng