Funtua: Sanata ya yi magana da shi daf da zai mutu, Saraki ya yi wa Buhari ta’aziyya

Funtua: Sanata ya yi magana da shi daf da zai mutu, Saraki ya yi wa Buhari ta’aziyya

Sanata Ben Murray-Bruce, tsohon Sanatan Najeriya, ya bayyana yadda ya yi magana a wayar salula da Malam Ismail Isa Funtua a daren da zai cika.

Tsohon sanatan Bayelsa, ya ke cewa ya yi waya da Ismaila Isa Funtua a ranar Litinin, har dattijon ya yi alkawarin kiransa a waya yau, sai kuma kawai ya ji labarin rasuwarsa.

Ben Murray-Bruce ya rubuta: “Na ji takaicin mutuwar ‘danuwana kuma babban abokin aiki, Mallam Isa Funtua. Na yi magana da shi sa’o’i uku rak kafin a ji labarin mutuwarsa, har ya yi mani alkawarin zai kira ni gobe.”

Sanata Murray-Bruce ya kara da cewa: “Ina addu’a Ubangiji ya ba iyallinsa da masoyansa hakuri, kuma Ubangiji ya sa ya huta.”

Bisa dukkan alamu, Ben Murray Bruce mai shekaru 64 a Duniya ya na cikin aminan marigayin kuma wanda su ka san juna a harkar aikin jarida da yada labarai.

Shekara guda kenan da ‘dan siyasar ya rasa mai dakinsa bayan sun shafe shekaru 41 su na zaman aure.

KU KARANTA: Shugaban kasa ya yi jawabi bayan mutuwar Ismail Funtua

Funtua: Sanata ya yi magana da shi daf da zai mutu, Saraki ya yi wa Buhari ta’aziyya
Marigayi Funtua da Sanata Saraki Hoto: Twitter
Asali: Twitter

Shi ma tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki ya yi magana bayan ya samun labarin rasuwar wannan Bawan Allah.

Saraki ya rubuta: “InnalilLahi Wa Inna Ilaehi Rajiun. Ina yi wa mai girma shugaban kasa Muhammadu Buhari GCFR ta’ziyyar mutuwar Alhaji Ismaila Isa Funtua."

Tsohon gwamnan ya ce: "A matsayinsa na abokin tafiyar marigayin mahaifina, Alhaji Funtua ya kasance mani wani tafki na hikima.”

“A ko yaushe a shirye ya ke ya bani shawarwarinsa da ra’ayoyi game da batutuwa. Zan yi kewansa, Najeriya ta rasa ‘dan kishin kasa kuma ya kasance tambarin hadin-kai.”

“Ina mika ta’aziyya ta ga iyali, abokai, mutane da gwamnatin jihar Katsina da kuma kasa baki daya. Ubangiji Allah SWT ya gafarta masa, ya ba shi gida a Aljannah Firdaus.” Inji Saraki

Funtua ya rike ministan harkokin ruwa a gwamnatin Shagari, a lokacin mahaifin Saraki watau Marigayi Olusola Saraki shi ne shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel