Har abada Gwamna Makinde ba zai kama kafar Ajimobi ba – Fatima Ganduje

Har abada Gwamna Makinde ba zai kama kafar Ajimobi ba – Fatima Ganduje

Fatima Ganduje-Ajimobi, ‘Diyar gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ta sa baki a game da rikicin da ya ke nema ya kaure bayan mutuwar mahaifin mijinta.

A makon da ya gabata ne tsohon gwamnan jihar Oyo watau Sanata Abiola Ajimobi ya rasu. Hajiya Fatima Ganduje-Ajimobi ta na auren ‘dansa Idris Abiola Ajimobi.

Tun da Abiola Ajimobi ya cika ake samun sabani tsakanin gwamnan jihar Oyo ta PDP da iyali da magoya bayan tsohon gwamnan.

A ranar Talata, 30 ga watan Yuni, 2020, Segun Awosanya wanda aka fi sani da @Segalink ya fito Twitter ya na yabon gwamnatin Oyo kan matakin da ta dauka bayan rasuwar Ajimobi.

Awosanya ya rubuta: “Ban san adadin mutanen da su ka yi murna da yadda Seyi Makinde, gwamnan jihar Oyo ya ki biyewa tarkon da ake nema a yi wa mutanen jihar Oyo ba.”

“Ni na ji dadi da ya gane manakisar da aka shirya” - @Segalink.

Mista Awosanya ya yi wannan magana ne a ranar Litinin da kimanin karfe 12:43. Washegari da yamma, sai Fatima Ganduje-Ajimobi ta maida masa martani ta shafinta na Twitter.

'KU KARANTA: 'Yar Tinubu ta na cikin wadanda za su sa ido wajen daukar Matasa aiki

Har abada Gwamna Makinde ba zai kama kafar Ajimobi ba – Fatima Ganduje
Fatima Ganduje da Idris Ajimobi
Asali: Twitter

A cewar Ganduje, Abiola Ajimobi ya sha gaban Injiniya Seyi Makinde, kuma gwamnan mai-ci, ba zai iya sa kafa a inda Marigayin ya taka ba.

‘Diyar gwamnan na Kano ta yi dariya ta ce: “Jirwaye ya na da hadari. SM (Seyi Makinde) ba zai taba zuwa ko da kusa da Ajimobi ba, har abada.”

Surukar tsohon gwamnan ta kara da cewa: “Ba sa’an ku ba ne!!!

Wasu sun fito su na sukar Ganduje kan tsoma baki cikin siyasar jihar Oyo da ba ta da ilmi a kai.

Wannan ne kusan karon farko da Fatima Ganduje-Ajimobi ta yi magana a Twitter, bayan ta fito ta karyata rade-radin da aka rika yi na mutuwar Ajimobi a lokacin da ya ke kwance a asibiti.

A makon jiya Bazawar marigayin ta samu kanta ta na cacar baki da mataimakin gwamnan jihar Oyo. Florence Ajimobi ta ce gwamnatin PDP ta sa siyasa a lamarin mutuwar mai gidanta.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel