Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 587 sun kamu da cutar Korona a Najeriya

Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 587 sun kamu da cutar Korona a Najeriya

Hukumar hana yaduwar Cututtuka a Najeriya watau NCDC ta sanar da cewa annobar cutar Korona ta sake harbin sabbin mutane 587 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11:18 na daren ranar Laraba, 17 ga watan Yuni na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 490 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-155

Edo-75

FCT-67

Rivers-65

Oyo-56

Delta-50

Bayelsa-25

Plateau-18

Kaduna-18

Enugu-17

Borno-12

Ogun-12

Ondo-7

Kwara-4

Kano-2

Gombe-2

Sokoto-1

Kebbi-1

17,735 sun kamu

5,967 aka sallama

469 sun mutu

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng