Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 587 sun kamu da cutar Korona a Najeriya
Hukumar hana yaduwar Cututtuka a Najeriya watau NCDC ta sanar da cewa annobar cutar Korona ta sake harbin sabbin mutane 587 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11:18 na daren ranar Laraba, 17 ga watan Yuni na shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 490 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;
Lagos-155
Edo-75
FCT-67
Rivers-65
Oyo-56
Delta-50
Bayelsa-25
Plateau-18
Kaduna-18
Enugu-17
Borno-12
Ogun-12
Ondo-7
Kwara-4
Kano-2
Gombe-2
Sokoto-1
Kebbi-1
17,735 sun kamu
5,967 aka sallama
469 sun mutu
Asali: Legit.ng