Saboda kokarin da Danbatta ya yi, na bukaci ya kara shekara 5 a NCC – Inji Pantami
Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Dr. Isa Ibrahim Ali-Pantami, ya bayyana dalilinsa na ba shugaban kasa Muhammadu Buhari shawarar sake nada farfesa Umar Danbatta a matsayin shugaban hukumar NCC.
Isa Ibrahim Ali-Pantami ya bayyana hakan ne a lokacin da shugabannin hukumar NCC su ka kawo masa ziyarar ban girma a ofishinsa. Ministan ya ce ya dauki matakin hakan ne domin ganin abubuwa sun daure a ma’aikatar.
Mai girma ministan ya yi wannan bayani ne a ranar Talata, 9 ga watan Yuni, 2020 kamar yadda mu ka samu labari daga jaridar Daily Nigerian.
Dr. Isa Ibrahim Ali-Pantami ya kuma bayyana cewa matakin da ya dauka ya na da nasaba da nasarorin da harkar sadarwa ta samu a cikin shekaru biyar da su ka wuce a dalilin kokarin da Umar Danbatta ya yi a hukumar NCC.
Duk da haka Pantami, ya yi magana game da bukatar shugabannin NCC su hada-kai su yi aiki tare da ma’aikatarsa da sauran hukumomi wajen ganin an cin ma burin da gwamnati ta yi niyya na NDEPS tsakanin shekarar 2020 zuwa 2025.
KU KARANTA: Shugaban kasa Buhari ya sake nada Danbatta a matsayin Shugaban NCC
Ministan ya kuma tunawa shugaban NCC cewa abin da ake bukata wurinsa shi ne ya bunkasa hanyoyin sadarwa da tattalin arzikin zamani, wanda bukatar hakan ta fi muhimmanci a yanzu bayan barkewar annobar cutar COVID-19.
“Nasarorin hukumar sun rataya ne a kan mu gaba daya. Yayin da mu a matsayinmu na ma’aikata, za mu yi bakin kokarinmu na kawo tsare-tsare, sannan kuma mu sa ido a kan ayyukan hukumar.”
An rahoto Dr. Pantami ya cigaba da cewa: “Ina kira ga gidan NCC su hada-kai, su ajiye duk bambanci, su tabbatar da adalci da gaskiya wajen duk matakan da za su dauka. Bugu da kari, su samu hadin-kai.”
Wadanda su ka takewa Danbatta baya sun hada da: Ubale Maska, Adewolu; Shu’aibu Ayuba; Yetunde Akinloye; Efosa Idehen. Sai kuma Dr. Henry Nkemadu; Mohammed Babajika, da Usman Mala.
Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Asali: Legit.ng