Covid-19: Sarkin Musulmi ya yi umurnin kowa yayi Sallar Idi a gida

Covid-19: Sarkin Musulmi ya yi umurnin kowa yayi Sallar Idi a gida

- Sarkin Musulmi ya bayyana matsayarsa a kan yadda za a yi sallar Idin shekarar nan

- A yayin da sarkin Musulmin yace musulmai su yi sallarsu a gida don gujewa cunkoso, wasu gwamnonin arewa sun dage dokarsu don a yi sallar a jam'i

- Sarkin musulmin yace sallar idin ba farilla bace kuma idan har akwai kalubalen tsaro da ya hada da lafiya ana hakura ne kwata-kwata

Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Sa'ad ya bayyana matsayarsa a kan yadda za a yi sallar Idin shekarar nan

Alh Sa'ad Abubakar, wanda shine shugaban majalisar koli ta al'amuran addinin Musulunci na kasa, ya bada umarnin cewa Musulmi su yi sallarsu a gida don dakile yaduwar cutar coronavirus.

Amma kuma, wasu gwamnonin arewa sun sassauta doka a jihohinsu don bai wa Musulmi damar yin sallar Idin a jam'i.

Sallar idi: An samu sabani tsakanin sarkin Musulmi da wasu gwamnonin arewa
Sallar idi: An samu sabani tsakanin sarkin Musulmi da wasu gwamnonin arewa Hoto: Vanguard
Asali: UGC

A farkon makon nan na gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya amince da a yi sallar Juma'a ta ranar 22 ga watan Mayu da kuma sallar Idi.

A ranar Laraba, gwamnan jihar Bauchi, Gwamna Bala Mohammed ya amince da yin sallar idi a jihar yayin da ya bukaci a kiyaye dokar nesa-nesa da juna tare da saka takunkumin fuska.

Sauran jihohin da suka bi ayari sun hada da Yobe, Jigawa, Gombe, Borno da Zamfara.

KU KARANTA KUMA: COVID-19: Sai mun kawo karshen dukkan damuwar Kanawa - Ganduje

A wata takarda da mataimakin sakataren majalisar koli ta al'amuran addinin Musulunci, Farfesa Salisu Shehu, ya fitar a ranar Litinin, 20 ga watan Mayu, ya ce "sallar Idi ba wajibi bace kuma ba a son yin ta matukar akwai wata barazana ta tsaro ko annoba."

"Musulmai su yi sallar idi amma yayin da suke kiyaye dokokin tsafta, saka takunkumin fuska da kuma nesa-nesa da juna."

"A wannan halin, ana bukatar a kiyaye taron jama'a ballantana irin na idi."

"Amma kuma a jihohi da ba a amince da yin sallar ba, ana kira ga Musulmi da su bi doka yayin da suka saka wa a ransu cewa niyyarsu za ta samar musu da lada."

*Mun sauya wasu abubuwa cikin labarin nan musamman bangarorin cewa gwamnoni sun samu sabani da Sarkin Musulmi. Ayi mana afuwa maganar ba haka take ba

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng