Bama-bamai sun tashi a jihar Borno
Rahotanni da Legit.ng ta samu daga wasu sanannun jaridun kasar nan sun bayyana cewa an samu fashewar bama - bamai a jihar Borno.
Jaridu, wadanda suka hada 'TheNation', gidan talabijin na TVC, SaharaReporters da sauransu, sun bayyana cewa bama - baman sun fashe ne a kauyen Konduga, lamarin da ya sa mazauna yankin gudun neman tsira da rayukansu.
SaharaReporters ta bayyana cewa bama - baman sun fashe ne da misalin karfe 8:38 na daren ranar Litinin.
A cewar SaharaReporters, wata majiya daga cikin jami'an tsaro ta sanar da ita cewa babu wani bayani a kan tashin bama - baman ko barnar da tashinsu ta haifar ya zuwa wanan lokaci.
Kazalika, majiyar ta ce mutane biyu sun mutu, kamar yadda SaharaReporters ta wallafa.
"An samu fashewar bama - bamai guda biyu a Mandirari Anguwan da misalin karfe 8:39 na daren an," a cewar majiyar SaharaReporters.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng