Bama-bamai sun tashi a jihar Borno

Bama-bamai sun tashi a jihar Borno

Rahotanni da Legit.ng ta samu daga wasu sanannun jaridun kasar nan sun bayyana cewa an samu fashewar bama - bamai a jihar Borno.

Jaridu, wadanda suka hada 'TheNation', gidan talabijin na TVC, SaharaReporters da sauransu, sun bayyana cewa bama - baman sun fashe ne a kauyen Konduga, lamarin da ya sa mazauna yankin gudun neman tsira da rayukansu.

SaharaReporters ta bayyana cewa bama - baman sun fashe ne da misalin karfe 8:38 na daren ranar Litinin.

A cewar SaharaReporters, wata majiya daga cikin jami'an tsaro ta sanar da ita cewa babu wani bayani a kan tashin bama - baman ko barnar da tashinsu ta haifar ya zuwa wanan lokaci.

Kazalika, majiyar ta ce mutane biyu sun mutu, kamar yadda SaharaReporters ta wallafa.

"An samu fashewar bama - bamai guda biyu a Mandirari Anguwan da misalin karfe 8:39 na daren an," a cewar majiyar SaharaReporters.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng