Yanzu Yanzu: Buhari ya bayyana Gambari a matsayin sabon shugaban ma’aikatan fadarsa, ya jagoranci zaman majalisar zartarwa

Yanzu Yanzu: Buhari ya bayyana Gambari a matsayin sabon shugaban ma’aikatan fadarsa, ya jagoranci zaman majalisar zartarwa

- Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tabbatar da Farfesa Ibrahim Gambari a matsayin shugaban ma’aikatansa

- Shugaban kasar da kansa ne ya tabbatar dashi a ranar Laraba, 13 ga watan Mayu

- Harma Gambari ya halarci zaman majalisa na farko a fadar shuaban kasa, Abuja

A karshe, fadar shugaban kasa ta tabbatar da Farfesa Ibrahim Gambari a matsayin sabon ma’aikatan shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Farfesa Gambari ya kama aiki a matsayin shugaban ma’aikatan Buhari bayan an gabatar da shi a gaban majalisar zartarwa lokacin ganawarta a ranar Laraba, 13 ga watan Mayu, Channels TV ta ruwaito.

Sakataren din-din-din na majalisar, Alhaji Tijani Umar, ya zaga da sabon shugaban ma’aikatan tarayyan don ganin gine-ginen fadar shugaban kasar.

Taron ya fara wurin karfe 11:22 na safe inda aka fara tattaunawa a kan annobar Coronavirus da ta addabi kasar nan, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

KU KARANTA KUMA: Tirkashi: 'Yan bindiga sun sace babban hafsin soja

An yi taron ne ta hanyar kiyaye dokar nesa-nesa da juna wacce ta zama doka ta farko da aka fara bi a taron.

An yi shiru na minti daya don karrama marigayi Malam Abba Kyari da wasu 'yan majalisar kafin a fara taron yayin da sakataren gwamnatin tarayya ya bayyana Gambari a matsayin sabon shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasar.

Gambari ya zauna a kujerar da aka tanada don shi wacce ke kusa da ta shugaban kasa Buhari bayan an gabatar da shi.

A baya mun ji cewa Sarkin Ilorin, Ibrahim Sulu-Gambari ya mika godiyarsa ga shugaban kasa Muhammadu Buhari a kan nada Ibrahim Gambari a matsayin sabon shugaban ma'aikatan fadarsa.

Gambari, wanda farfesan kimiyyar siyasa ne kuma tsohon wakilin Najeriya a majalisar dinkin duniya dan asalin jihar Kwara ne.

A wata takarda da ta fita a ranar Laraba, Sulu-Gambari ya kwatanta nadin da babban karramawa ga jama'ar Ilorin da Kwara gaba daya.

Ya ce zaben Gambari a wannan matsayin zai bayyanar da kwarewarsa tare da gogewarsa a fannin mulkin wanda zai kasance babbar gudumawa ga gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng