Buhari ya nada Mohammad Shehu a matsayin sakataren RMAFC

Buhari ya nada Mohammad Shehu a matsayin sakataren RMAFC

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya amince da nadin Mohammed Bello Shehu, a matsayin sakataren hukumar kasafin kudaden haraji da gwamnatin tarayya ta samu.

Shehu, wanda nadinsa ya fara aiki a ranar 19 ga watan Maris, zai shafe zangon farko mai wa'adin shekaru biyar a hukumar RMAFC tare da zabin sabunta nadinsa a zango na biyu idan shugaban kasa ya ga dama.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Willie Bassey, darektan yada labarai a ofishin sakataren gwamnatin tarayya. Sanarwar ta fito ne da yammacin ranar Litinin.

A cewar sanarwar, shugaba Buhari ya sake amincewa da nadin Bitrus Danharbi Chinoko a matsayin babban darektan CMD (Centre for Management Development) Lagos.

Nadinsa zai fara aiki daga ranar 27 ga watan Afrilu.

Buhari ya nada Mohammad Shehu a matsayin sakataren RMAFC
Buhari
Asali: Twitter

Kafin nadinsa a matsayin babban darekta mai cikakken iko, Mista Chinoko ya kasance mukaddashin babban darektan CMD.

DUBA WANNAN: Jami'an tsaro sun kashe 'yan Najeriya 11 bayan tsawaita dokar kulle - NHRC

"Shugaba Buhari ya tayasu murna tare da bukatar su yi amfani da kwarewarsu domin kawo sauye - sauye masu amfani da muhimmanci a hukumomin da zasu jagoranta," a cewar sanarwar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel