Korona: Ta harbi karin mutane 381, 55 a Kano, 44 a Jigawa, 19 a Bauchi

Korona: Ta harbi karin mutane 381, 55 a Kano, 44 a Jigawa, 19 a Bauchi

Hukumar yaki da cututtuka ma su yaduwa a kasa (NCDC) ta ce annobar cutar covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 381 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11:20 na daren ranar Alhamis, 07 ga watan Mayu, 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta sanar da cewa karin sabbin mutane 381 din sun fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

183-Lagos

55-Kano

44-Jigawa

19-Zamfara

19-Bauchi

11-Katsina

9-Borno

8-Kwara

7-Kaduna

6-Gombe

5-Ogun

4-Sokoto

3-Oyo

3-Rivers

2-Niger

1-Akwa Ibom

1-Enugu

1-Plateau

Alkaluman NCDC na ranar Alhamis sun nuna cewa an samu hauhawar lambobin mutanen da suka kamu da cutar a jihohin arewacin Najeriya, musamman jihohin arewa maso yamma da arewa maso gabas.

NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:20 na daren ranar Alhamis, 07 ga watan Mayu, akwai jimillar mutane 3526 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a fadin Najeriya.

DUBA WANNAN: An bawa hammata iska a kan gawar mahaifiyar Buratai

An sallami mutane 601 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 107.

Daga cikin mutanen da aka sallama akwai mutane 16 da suka warke sarai bayan sun yi jinyar cutar a cibiyar killacewa da ke Kano.

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Muhammed Garba, ya tabbatar da sallamar mutanen a cikin wani jawabi da ya fitar da yammacin ranar Alhamis.

Daga cikin mutanen da aka sallama akwai Farfesa Abdulrazak Garba Habeeb na sashen koyar da aikin likita a jami'ar Bayero da kwamishinan lafiya na jihar Kano, Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng