Korona ta hallaka likita a jihar Borno
Wani kwararren likita ya mutu a asibitin koyarwa (UMTH) na jami'ar Maiduguri bayan ya kamu da kwayar cutar covid a jihar Borno, kamar yadda SaharaReporters ta rawaito.
Kwararren likitan mai suna Mohammed Kumshe ya mutu ne ranar Alhamis a bangaren killace masu jinyar korona a asibitin.
SaharaReporter ta bayyana cewa likitan ya kamu da kwayar cutar ne bayan ya yi mu'amala da wani mai cutar.
Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa a kasa (NCDC) ta ce ya zuwa yanzu akwai jimillar mutane 116 da aka tabbatar suna dauke da kwayar cutar a jihar Borno.

Asali: UGC
Daga jihar Yobe, mai makwabtaka da jihar Borno, wasu manyan mutane uku da suka yi suna sun mutu a cikin sa'a 24 daga cutar da ake zargin cewa annobar korona ce jihar Yobe, kamar yadda SaharaReporters ta rawaito.
Manyan mutane sune; tsohon mamba mai wakiltar Nguru/Machina/Karasuwa/Yusufari a majlisar wakilai ta kasa, Alhaji Baba Bukar Machina, Muazu Buraji, darektan ma'aikatar lafiya ta jihar Yobe, da Alhaji Bana Kura, wani sanannen ma'aikacin gwamnati a Geidam.
Machina ya mutu ne a cibiyar killacewa a Damaturu, babban birnin jihar Yobe, kuma za a binne shi ranar Alhamis.
DUBA WANNAN: An bawa hammata iska a kan gawar mahaifiyar Buratai
Da SaharaReporters ta tuntubi Mamman Mohammed, darektan yada labarai da kafafen sadarwa a Yobe, ya ce bashi da masaniya a kan abinda ya ke faruwa,
Ya bayyana cewa kwamishinan lafiya na Yobe zai gabatar da jawabi ga manema labarai a kan halin da ake ciki a jihar.
A ranar Laraba ne Legit.ng ta wallafa rahoton cewa a kalla mutum 155 ne su ka mutu a cikin kwanaki 6 a kananan hukumomin Gashua da Potiskum da ke jihar Yobe.
A cewar jaridar SaharaReportes, mutanen na nuna alamu da ke kama da na ma su dauke da kwayar cutar covid-19 kafin su mutu.
Yawaitar mace - macen, wacce ke kama da irinta jihar Kano, ta jefa tsoro da zaman zulumi a tsakanin mazauna kananan hukumomin.
Wani kwamitin bincike da shugaban kasa ya tura Kano ya alakanta yawaitar mutuwar mutanen jihar da annobar covid-19.
Wata majiya ta sanar da SaharaReporters cewa a kalla mutane 98 ne su ka mutu a karamar hukumar Potiskum a tsakanin ranar Alhamis, 30 ga watan Afrilu, zuwa ranar Talata, 5 a watan Mayu.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng