Korona ta hallaka likita a jihar Borno

Korona ta hallaka likita a jihar Borno

Wani kwararren likita ya mutu a asibitin koyarwa (UMTH) na jami'ar Maiduguri bayan ya kamu da kwayar cutar covid a jihar Borno, kamar yadda SaharaReporters ta rawaito.

Kwararren likitan mai suna Mohammed Kumshe ya mutu ne ranar Alhamis a bangaren killace masu jinyar korona a asibitin.

SaharaReporter ta bayyana cewa likitan ya kamu da kwayar cutar ne bayan ya yi mu'amala da wani mai cutar.

Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa a kasa (NCDC) ta ce ya zuwa yanzu akwai jimillar mutane 116 da aka tabbatar suna dauke da kwayar cutar a jihar Borno.

Korona ta hallaka likita a jihar Borno
Marigayi Mohammed Kumshe Hoto: SaharaReporters
Asali: UGC

Daga jihar Yobe, mai makwabtaka da jihar Borno, wasu manyan mutane uku da suka yi suna sun mutu a cikin sa'a 24 daga cutar da ake zargin cewa annobar korona ce jihar Yobe, kamar yadda SaharaReporters ta rawaito.

Manyan mutane sune; tsohon mamba mai wakiltar Nguru/Machina/Karasuwa/Yusufari a majlisar wakilai ta kasa, Alhaji Baba Bukar Machina, Muazu Buraji, darektan ma'aikatar lafiya ta jihar Yobe, da Alhaji Bana Kura, wani sanannen ma'aikacin gwamnati a Geidam.

Machina ya mutu ne a cibiyar killacewa a Damaturu, babban birnin jihar Yobe, kuma za a binne shi ranar Alhamis.

DUBA WANNAN: An bawa hammata iska a kan gawar mahaifiyar Buratai

Da SaharaReporters ta tuntubi Mamman Mohammed, darektan yada labarai da kafafen sadarwa a Yobe, ya ce bashi da masaniya a kan abinda ya ke faruwa,

Ya bayyana cewa kwamishinan lafiya na Yobe zai gabatar da jawabi ga manema labarai a kan halin da ake ciki a jihar.

A ranar Laraba ne Legit.ng ta wallafa rahoton cewa a kalla mutum 155 ne su ka mutu a cikin kwanaki 6 a kananan hukumomin Gashua da Potiskum da ke jihar Yobe.

A cewar jaridar SaharaReportes, mutanen na nuna alamu da ke kama da na ma su dauke da kwayar cutar covid-19 kafin su mutu.

Yawaitar mace - macen, wacce ke kama da irinta jihar Kano, ta jefa tsoro da zaman zulumi a tsakanin mazauna kananan hukumomin.

Wani kwamitin bincike da shugaban kasa ya tura Kano ya alakanta yawaitar mutuwar mutanen jihar da annobar covid-19.

Wata majiya ta sanar da SaharaReporters cewa a kalla mutane 98 ne su ka mutu a karamar hukumar Potiskum a tsakanin ranar Alhamis, 30 ga watan Afrilu, zuwa ranar Talata, 5 a watan Mayu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng