Kasashe 5 da cutar korona ta bulla amma ba a rasa rai ba

Kasashe 5 da cutar korona ta bulla amma ba a rasa rai ba

Zuwa ranar yau Laraba, 6 ga watan Mayu, a kalla mutum miliyan 3.6 suka kamu da cutar coronavirus a fadin duniya. An samu warakar mutum 1.2 amma an rasa rayuka 252,000 a fadin duniya.

Tun bayan bullowar cutar a Najeriya, mutum 2,950 ne suka kamu da cutar yayin da mutum 481 ne suka warke daga jinyar cutar. Mutum 98 ne suka rasa rayukansu.

Cutar sarkewar numfashin wacce aka fara samu a garin Wuhan a kasar China ta bulla a kalla kasashe 180 na duniya.

Covid-19: Kasashe 5 da cutar korona ta bulla amam ba a rasa rai ba
Covid-19: Kasashe 5 da cutar korona ta bulla amam ba a rasa rai ba
Asali: UGC

Akwai wasu kasashen da har yanzu ba a samu bullar cutar ba amma kuma wasu har ta bulla bata kashe ko rai daya ba. Ga wasu daga cikin kasashen.

KU KARANTA KUMA: Matafiya 4 cikin 11 da aka damke za su shiga kudu daga Sokoto suna dauke da Korona

1. Tsibirin Falkland: An tabbatar da cewa mutum 13 sun kamu da cutar amma duk sun warke.

2. Greenland Greelnad: Ita ce kasa mai tsibiri mafi girma a duniya. Tana tsakanin kogin Arctic da na Atlantic. Mutum 11 ne suka kamu amma duk sun warke. Har yanzu kuwa ba a sake samun mai cutar a kasar ba.

3. Papua New Guinea: Cutar ta harba mutum 8 amma dukkansu sun warke. Kasar na kudu maso yay kogin Pacific. An fara samun bullar cutar a kasar a ranar 20 ga watan Maris.

4. Saint Barthelemy: Kasar ta tabbatar da kamuwar mutum 6 da cutar amma duk sun warke a halin yanzu. Tsibiri ne wanda aka fi sani da St. Barts. Yana da gabobin ruwa da kuma shaguna masu matukar bada sha'awa.

5. Anguilla: Kasar ta tabbatar da kamuwar mutum 3 da muguwar cutar amma a halin yanzu duk sun warke. Kasar na nahiyar Amurka ta Arewa.

A wani labarin kuma, ministan lafiya, Dakta Osagie Ehanire, ya ce Najeriya ta fara amfani da wani magani mai suna 'remdesivir' a kan ma su jinyar cutar covid-19.

Da ya ke gabatar da jawabi a gaban mambobin majalisar wakilai ranar Talata, Ehanire ya ce da maganin ake amfani a kan ma su jinyar cutar covid-19 jihar Legas.

Sai dai, ministan bai bayyana irin tasirin maganin a kan cutar covid-19 ba.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng