Bayanai sun fito a kan musabbabin mutuwar babban sarki a Zamfara

Bayanai sun fito a kan musabbabin mutuwar babban sarki a Zamfara

Da safiyar ranar Lahadi ne Legit.ng ta wallafa labarin mutuwar Sarkin masarautar Kauran Namoda a jihar Zamfara, Alhaji Muhammad Ahmad Asha.

Sarkin ya rasu ne da safiyar ranar Lahadi, 3 ga watan Mayun 2020 bayan fama da gajeriyar rashin lafiya kamar yadda wani na kusa da fadar sarkin ya tabbatar wa BBC.

Ya rasu yana da shekaru 71 a duniya, ya kuma bar mata uku da yaya da dama.

A cewar jaridar The Punch, Sarkin ya mutu ne a asibitin da aka killace shi.

Jaridar ta ce ya ana zargin cewa cutar covid-19 ce ta yi sanadin mutuwarsa.

The Punch ta ce sakataren yada labarai na kwamitin yaki da cutar covid-19 a jihar Zamfara, Mustafa Jafaru, ya ce basaraken ya na killace ne a asibitin kwararru da ke garin Gusau, babban birnin jiha.

Jafaru ya bayyana cewa an dauki jininsa tare da aika shi zuwa dakin gwaji a Abuja, amma har ya zuwa wannan lokaci ana dakon fitowar sakamakon gwajin.

Bayanai sun fito a kan musabbabin mutuwar babban sarki a Zamfara
Bayanai sun fito a kan musabbabin mutuwar babban sarki a Zamfara
Asali: UGC

Ya kara da cewa har yanzu gawar Sarkin ta na asibitin, yayin da ake jiran yi ma sa jana'iza.

DUBA WANNAN: 'A fusace na ke a lokacin' - Dattijon da aka kama saboda ya zagi Buhari ya yi bayani

Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Sani Yariman Bakura, ne ya nada marigayin a matsayin sarkin masarautar Kauran Namoda na 71 a shekarar 2004.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng