Hana fita: Kungiyar AYCF ta caccaki Sanwo-Olu a kan watsi da yan Arewa wajen rabon tallafi

Hana fita: Kungiyar AYCF ta caccaki Sanwo-Olu a kan watsi da yan Arewa wajen rabon tallafi

- Kungiyar AYCF ta caccaki gwamnatin Lagas a kan rabon kayan rage radadin dokar hana fita a jahar

- Kungiyar ta hannun shugabanta na kasa, Yerima Shettima, ta ce an bar yan Arewa a Lagas a baya kwata-kwata wajen rabon kayan tallafin

- Shettima ya bayyana matakin gwamnatin jahar a matsayin rashin wayewa kuma ba mai karbuwa ba

Kungiyar matasan Arewa (AYCF) ta caccaki gwamnatin jahar Lagas a kan watsi da ta yi da al’ummanta a jahar wajen rabon kayan rage radadin hana fita.

A wata sanarwa da shugabanta na kasa, Alhaji Yerima Shettima ya aike wa Legit.ng, kungiyar ta ce tana sane da cewar an bar al’umman Lagas a baya kwata-kwata wajen rabon kayan tallafin.

Shettima ya bayyana cewa kungiyar na jin radadin halin bakin ciki da mutanenta ke ciki a jahar na watsi da aka yi da su.

Hana fita: Kungiyar AYCF ta caccaki Sanwo-Olu a kan watsi da yan Arewa wajen rabon tallafi
Hana fita: Kungiyar AYCF ta caccaki Sanwo-Olu a kan watsi da yan Arewa wajen rabon tallafi
Asali: Original

Ya bayyana cewa kayan tallafin ba kyauta bane illa hakkin dukkanin mutane da ke jahar, ba tare da la’akari da yankin da suka fito ba a kasar.

KU KARANTA KUMA: Coronavirus: Jerin jihohi 34 a Najeriya da cutar ta bulla da adadin wadanda suka kamu a kowace jiha

Shetimma ya kuma bayyana cewa hakan rashin wayewa ne, da rashin tunani kuma ba za a yarda gwamnatin Lagas ta yi watsi da yan Arewa ba a wannan lokaci da ake tsananin bukata.

A wani labarin kuma, jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a jahar Kaduna, ta caccaki Gwamna Nasir El-Rufai a kan tsawaita dokar hana fita na sa’o’i 24 da ya yi a jahar zuwa tsawon wani wata guda.

Jam’iyyar ta yi zargin cewa abun da ya fi damun gwamnatin jahar shine kudaden shiga da za ta samu daga tarar da wadanda suka saba dokar fitan za su biya.

PDP, yayin da ta ke caccakar tsarin yadda gwamnatin jahar ke bi wajen hana yaduwar annobar ta COVID-19, ta ce gwamnati mai mulki ba ta yi wa al’umma karin haske kan irin nasara da ake samu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng