Coronavirus: Muna rokon Buhari ya kawo dauki jihar Kano - Ganduje

Coronavirus: Muna rokon Buhari ya kawo dauki jihar Kano - Ganduje

Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya kirayi gwamnatin tarayya da ta kawo masa dauki na tunkarar annobar cutar coronavirus a jihar.

A rahoton da jaridar Daily Trust ta ruwaito, Ganduje ya mika kokon barar neman tallafin kudi da kuma kayan agaji domin dakile bazuwar cutar corona a jihar da ke Arewacin Najeriya.

Ganduje ya shigar da wannan koke yayin da shugaban cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta Najeriya NCDC, Dr. Chikwe Ihekweazu ya ziyarci fadar gwamnatin Kano a ranar Talata.

Gwamnan wanda ake yiwa lakabi da Khadimul Islama, ya ce a yayin da jihar ke ci gaba da tunkarar annobar corona, basu samu wani tallafi ba daga bangaren gwamnatin tarayya.

Duk da cewa ba a samu bullar cutar ba a yankunan karkara ko kuma wajen birnin Kano, Ganduje ya ce dole a kasance cikin shirin tunkarar lamarin a duk sa'ilin da labari ya sha ban-ban.

Ganduje ya ce muddin aka samu bullar cutar a yankunan karkara na jihar, to kuwa babu shakka akwai kalubale babba da zai rataya a wuyan gwamnatinsa doriya a kan wanda ta ke fuskanta yanzu.

Ya ke cewa, "kawo yanzu ba mu da wata babbar matsala a jihar, amma akwai bukatar mu kasance cikin shiri."

Gwamnan Kano - Abdullahi Umar Ganduje
Gwamnan Kano - Abdullahi Umar Ganduje
Asali: Facebook

"Muna bukatar karin cibiyar gwaji a jihar, muna bukatar motocin jigilar marasa lafiya da ma'aikatan lafiya gami da na'urorin kariya, muna bukatar tallafin gaske domin tunkarar matsalolin mu cikin gaggawa."

"Kano ce ta uku a jerin jihohi mafi yawan mutanen da cutar corona ta harba baya ga kasancewar ta jiha mafi yawan al'umma a fadin kasar nan. Saboda haka muna bukatar tallafin kudi daga gwamnatin tarayya,” inji shi.

KARANTA KUMA: Mutanen da cutar coronavirus ta kashe sun haura 170,000 a duniya - Alkalumma

A nasa bangaren, Dr Ihekweazu ya ce tawagarsa ta ziyarci jihar Kano ne domin jaddada goyon bayan gwamnatin tarayya a fagen yaki da annobar cutar corona.

Ya yaba da kokarin da gwamnatin Kano ke yi wajen dakile bazuwar cutar a jihar.

Shugaban na NCDC ya ce karuwar cutar covid-19 a jihar Kano ba abin mamaki bane idan akayi la'akari da yawan al'ummar da jihar ta kunsa.

Tun bayan bullar cutar karo na farko a jihar kwanaki goma da suka gabata, an samu mutane 59 da suka harbu yayin da rai ya yiwa mutum daya halinsa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel