Coronavirus: Muna rokon Buhari ya kawo dauki jihar Kano - Ganduje

Coronavirus: Muna rokon Buhari ya kawo dauki jihar Kano - Ganduje

Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya kirayi gwamnatin tarayya da ta kawo masa dauki na tunkarar annobar cutar coronavirus a jihar.

A rahoton da jaridar Daily Trust ta ruwaito, Ganduje ya mika kokon barar neman tallafin kudi da kuma kayan agaji domin dakile bazuwar cutar corona a jihar da ke Arewacin Najeriya.

Ganduje ya shigar da wannan koke yayin da shugaban cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta Najeriya NCDC, Dr. Chikwe Ihekweazu ya ziyarci fadar gwamnatin Kano a ranar Talata.

Gwamnan wanda ake yiwa lakabi da Khadimul Islama, ya ce a yayin da jihar ke ci gaba da tunkarar annobar corona, basu samu wani tallafi ba daga bangaren gwamnatin tarayya.

Duk da cewa ba a samu bullar cutar ba a yankunan karkara ko kuma wajen birnin Kano, Ganduje ya ce dole a kasance cikin shirin tunkarar lamarin a duk sa'ilin da labari ya sha ban-ban.

Ganduje ya ce muddin aka samu bullar cutar a yankunan karkara na jihar, to kuwa babu shakka akwai kalubale babba da zai rataya a wuyan gwamnatinsa doriya a kan wanda ta ke fuskanta yanzu.

Ya ke cewa, "kawo yanzu ba mu da wata babbar matsala a jihar, amma akwai bukatar mu kasance cikin shiri."

Gwamnan Kano - Abdullahi Umar Ganduje
Gwamnan Kano - Abdullahi Umar Ganduje
Asali: Facebook

"Muna bukatar karin cibiyar gwaji a jihar, muna bukatar motocin jigilar marasa lafiya da ma'aikatan lafiya gami da na'urorin kariya, muna bukatar tallafin gaske domin tunkarar matsalolin mu cikin gaggawa."

"Kano ce ta uku a jerin jihohi mafi yawan mutanen da cutar corona ta harba baya ga kasancewar ta jiha mafi yawan al'umma a fadin kasar nan. Saboda haka muna bukatar tallafin kudi daga gwamnatin tarayya,” inji shi.

KARANTA KUMA: Mutanen da cutar coronavirus ta kashe sun haura 170,000 a duniya - Alkalumma

A nasa bangaren, Dr Ihekweazu ya ce tawagarsa ta ziyarci jihar Kano ne domin jaddada goyon bayan gwamnatin tarayya a fagen yaki da annobar cutar corona.

Ya yaba da kokarin da gwamnatin Kano ke yi wajen dakile bazuwar cutar a jihar.

Shugaban na NCDC ya ce karuwar cutar covid-19 a jihar Kano ba abin mamaki bane idan akayi la'akari da yawan al'ummar da jihar ta kunsa.

Tun bayan bullar cutar karo na farko a jihar kwanaki goma da suka gabata, an samu mutane 59 da suka harbu yayin da rai ya yiwa mutum daya halinsa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng