Yanzu-yanzu: Ofishin babban bankin Najeriya CBN ta kama da wuta

Yanzu-yanzu: Ofishin babban bankin Najeriya CBN ta kama da wuta

Labarin dake shigo mana da duminsa na nuna cewa ana gobara a ofishin babban bankin Najeriya CBN, reshen Jos, jihar Plateau a ranar Talata, 21 ga Afrilu, 2020.

Bankin ta tabbatar da hakan a shafinta na Tuwita inda ta bayyana cewa tuni an kashe wutar.

Jawabin yace “An samu karamin gobara a reshen babbar bankin Najerya dake Jos kuma an dakile ta a yau 21 ga Afrilu, 2020.“

KU KARANTA Mutanen da cutar coronavirus ta kashe sun haura 170,000 a duniya - Alkalumma

Wannan shine karo na hudu da manyan ofishohin gwamnatin tarayya a Abuja ke gobara duk da cewa babu maaikata a ofishohin.

An umurci maaikatan gwamnati suyi zamansu a gida saboda dokar ta bacin da gwamnatin tarayya ta sanya a Abuja.

A ranar 17 ga Afrilu, edkwatar hukumar gudanar da zabe ta kasa watau INEC dake birnin tarayya Abuja ta ci bal-bal kuma anyi asarar dukiyoyin gwamnati.

A ranar Larabar, 14 ga watan Afrilu 2020, gobara ta tashi a hedikwatar hukumar yi wa kasuwanci rijista ta kasa (CAC) da ke unguwar Maitama a birnin tarayya, Abuja.

Gobarar ta babbake hawa na karshe a ginin ofishin hukumar CAC mai bene hawa bakwai, tare da lalata muhimman kayayyaki.

Hakazalika a makonni biyu da suka wuce, gobara ta lashe ofishin akawunta janar na tarayya wacce akafi sani da baitul malin gwamnati dake Abuja.

Bayan gobarar ta kwashe lokaci tana ci bal-bal karamin ministan kasafi da tsare-tsare na kasa, Prince Clem Agba, ya yi magana a kan gobarar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng