Yanzu-yanzu: Ofishin babban bankin Najeriya CBN ta kama da wuta
Labarin dake shigo mana da duminsa na nuna cewa ana gobara a ofishin babban bankin Najeriya CBN, reshen Jos, jihar Plateau a ranar Talata, 21 ga Afrilu, 2020.
Bankin ta tabbatar da hakan a shafinta na Tuwita inda ta bayyana cewa tuni an kashe wutar.
Jawabin yace “An samu karamin gobara a reshen babbar bankin Najerya dake Jos kuma an dakile ta a yau 21 ga Afrilu, 2020.“
KU KARANTA Mutanen da cutar coronavirus ta kashe sun haura 170,000 a duniya - Alkalumma
Wannan shine karo na hudu da manyan ofishohin gwamnatin tarayya a Abuja ke gobara duk da cewa babu maaikata a ofishohin.
An umurci maaikatan gwamnati suyi zamansu a gida saboda dokar ta bacin da gwamnatin tarayya ta sanya a Abuja.
A ranar 17 ga Afrilu, edkwatar hukumar gudanar da zabe ta kasa watau INEC dake birnin tarayya Abuja ta ci bal-bal kuma anyi asarar dukiyoyin gwamnati.
A ranar Larabar, 14 ga watan Afrilu 2020, gobara ta tashi a hedikwatar hukumar yi wa kasuwanci rijista ta kasa (CAC) da ke unguwar Maitama a birnin tarayya, Abuja.
Gobarar ta babbake hawa na karshe a ginin ofishin hukumar CAC mai bene hawa bakwai, tare da lalata muhimman kayayyaki.
Hakazalika a makonni biyu da suka wuce, gobara ta lashe ofishin akawunta janar na tarayya wacce akafi sani da baitul malin gwamnati dake Abuja.
Bayan gobarar ta kwashe lokaci tana ci bal-bal karamin ministan kasafi da tsare-tsare na kasa, Prince Clem Agba, ya yi magana a kan gobarar.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng