Coronavirus: Gwamna Zulum ya rufe jahar Borno na tsawon kwanaki 14

Coronavirus: Gwamna Zulum ya rufe jahar Borno na tsawon kwanaki 14

- Gwamna Babagana Zulum, ya yi umurnin rufe jahar Borno na tsawon kwanaki 14

- Hakan na daga cikin kokarin da gwamnatin ke yi na hana yaduwar annobar COVID-19 a jahar

- Ya ce a wannan lokaci ana bukatar mutanen jahar su kasance a gida, sannan a rufe duk wani harkoki na kasuwanci da sauransu

Gwamnan jahar Borno, Umara Babagana Zulum, a ranar Litinin, 20 ga watan Afrilu, ya yi umurnin rufe jahar a wani kokari na hana yaduwar annobar coronavirus a jahar.

A wani jawabi na fadin jahar, Zulum ya ce: “Da karfin ikon da aka bani, na sa hannu a wani oda, wanda ke kaddamar da Covid-19 a matsayin cuta mai hatsari.“

"Don haka, na yi umurnin rufe jahar wanda zai haramta duk wani zirga-zirga a jahar Borno na tsawon kwanaki 14, fara daga karfe 10:30 na safiyar ranar Laraba, 22 ga watan Afrilu, 2020.“

"Dukkanin al’umman jahar Borno su kasance a gidajensu. Hakan na nufin hana duk wani zirga-zirga, yayinda za a rufe dukkanin ofishoshi da kasuwanci a jahar Borno a wannan lokacin. “

“An sanar da hukumomin tsaro kan dokar."

Coronavirus: Gwamna Zulum ya rufe jahar Borno na tsawon kwanaki 14
Coronavirus: Gwamna Zulum ya rufe jahar Borno na tsawon kwanaki 14
Asali: Twitter

Gwamnati za tayi amfani da wannan lokaci na hana zirga-zirga wajen ganowa da killace mutanen da suka yi mu’amala da mutum na farko da aka samu da cutar.

KU KARANTA KUMA: Gwamnan Borno ya jagoranci Tawaga sun ziyarci Dangin Abba Kyari a Bama

Sai dai kuma, kwamitin jahar kan kula da hana yaduwar COVID-19 ya gano mutane 97 da suka yi hulda da mai cutar wanda ya mutu.

Shugaban kwamitin, Alhaji Umar Kadafur, wanda ya kuma kasance mataimakin gwamnan jahar, ne ya bayyana hakan a taron manema labarai a Maiduguri.

A wani labari na daban, mun ji cewa marasa lafiyar da ke ziyartar wasu asibitoci ma su zaman kansu a jihar Legas sun samu sakonnin bukatar su killace kansu saboda su na cikin hatsarin kamuwa da kwayar cutar covid-19.

Asibitocin da yanzu gwamnatin jihar ta rufesu sune kamar haka; St Nicholas, reshen Lagos Island branch; First Cardiology Consultants Hospital da ke Ikoyi, inda Abba Kyari ya mutu, da St Edwards Hospital da ke Ajah.

Sauran sune; Vedic Lifecare Hospital da ke Lekki; County Hospital, Ogba da Premier Specialist Hospital da ke Victoria Island.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel