Yan Najeriya 3 sun mutu sakamakon COVID-19 a Amurka

Yan Najeriya 3 sun mutu sakamakon COVID-19 a Amurka

Benaoyagha Okoyen, karamin jakadan Najeriya a Birtaniya, ya tabbatar da mutuwar yan Najeriya uku wadanda suka kamu da cutar Coronavirus a kasar Amurka.

A bisa ga kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) Okoyen ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya saki.

Wadanda suka mutun sun hada da wani likita daga Abia, Bassey Offiong mai shekara 25 da kuma wata yar shekara 60.

Yan Najeriya 3 sun mutu sakamakon COVID-19 a Amurka
Yan Najeriya 3 sun mutu sakamakon COVID-19 a Amurka
Asali: UGC

“Mutum na farko ta kasance Hajia Laila Abubakar Ali mai shekara 60 daga Kano, wacce ta rasu a ranar 25 ga watan Maris yayinda ta ke samun kulawar likita a asibitin Lincoln da ke Bronx, New York.

"Na biyun, Bassey Offiong mai shekara 25 daga Calabar, dalibin ajin karshe da ke karantar Injiniya a jami’ar Western Michigan, Kalamazoo, ya rasu a ranar Asabar, 28 ga watan Maris, a asibitin Beaumont da ke Royal Oak.

"Sai na karshen ya kasance likita, Dr Celeb Anya, daga Ohafia a jahar Abia,” in ji sanarwar.

“Ya rasu yayinda ya ke yiwa al’umma hidima a wajen yaki da annobar COVID-19 a New York a ranar 1 ga watan Afrilu.

“A madadin jakadan Najeriya a New York, Ina mika ta’aziyya ya iyalan yan Najeriyar da suka mutu a mummunan lamarin.”

Ya kuma yaba ma ayyukan likitocin Najeriya a USA da suka yi kokari yaki da hana yaduwar cutar Coronavirus.

KU KARANTA KUMA: Saba dokar hana fita: Jami'an tsaro sun damke motoci 51, babura 46 a Abuja

A wani rahoton mun ji cewa, Cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karin mutane goma (10) da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Lahadi, 5 ga Afrilu, 2020.

Cibiyar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita inda tace: “An tabbatar da mutane goma(10) sun kamu da #COVID19 a Najerya, 8 a Legas, 2 a Abuja, 2 a Edo.

“Kawo karfe 1:15 na ranar 5 ga Afrilu, mutane 224 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami mutane 27 , kuma mutane 5 a rigamu gidan gaskiya.“

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng