Covid-19: Gwamnatin Bauchi ta saka dokar hana zirga-zirga na kwanaki 14 a jahar

Covid-19: Gwamnatin Bauchi ta saka dokar hana zirga-zirga na kwanaki 14 a jahar

Gwamnatin jahar Bauchi ta sanya dokar hana zirga-zirga na tsawon kwanaki 14 a fadin jahar daga cikin kokarinta na hana yaduwar cutar coronavirus a jahar.

Hakan ya biyo bayan samun karin wani mutum da ya kamu da cutar ta covid-19 a jahar a ranar Talata.

Mutumin da ya kamu da cutar na da shekaru 57 sannan har an aika dashi asibitin koyarwa na Jami’ar Tafawa Balewa domin a ci gaba da kulawa da shi, jaridar Premium Times ta ruwaito.

Gwamna Bala Mohammed na daya daga cikin mutane uku din da suka kamu da cutar a jahar.

Gwamna Bala Mohammed da ke kwance a asibiti ya Sanar da dokar hana walwala a jahar yana mai cewa dokar zai fara aiki ne ranar Alhamis, 2 ga watan Afrilu, da karfe 6:00 na yamma. Sannan cewa za a rufe dukkanin iyakokin jahar.

Covid-19: Gwamnatin Bauchi ta saka dokar hana zirga-zirga na kwanaki 14 a jahar
Covid-19: Gwamnatin Bauchi ta saka dokar hana zirga-zirga na kwanaki 14 a jahar
Asali: Facebook

Hakazalika domin rage wa mutane wahalan talauci yayin da suke zaman gida za a sassauta dokar a ranar Asabar da Laraba na kowace mako daga karfe 10:00 na safe zuwa 4:00 na yamma saboda su rika fita domin siyan kayan abinci da kayan da za su bukata.

Duk masu harkoki da ya shafi al’umma ba za su zauna a gida ba.

Gwamnati ta yi kira ga mutane da su ga wannan mataki da gwamnati ta dauka a matsayin hanyar dakile yaduwar coronavirus a jahar.

KU KARANTA KUMA: Sakamakon gwaji ya nuna Ganduje da matarsa basa dauke da cutar Covid-19

A wani labari na daban mun ji cwa wasu masallata da adadin su ya dara 25 sun kai wa jami'an kwamitin kar ta kwana na hana yaduwar kwayar cutar Covid-19 na jihar Legas hari a babban masallacin unguwar Agege a yayin da jami'an suka ziyarci masallacin domin tabbatar da cewa mutanen suna bin dokar da gwamnatin jihar ta saka.

A wani rahoto da ta wallafa a shafinta na Twitter @followlasg, gwamnatin jihar Legas ta yi Allah wadai da halin da matasan suka nuna na saba dokar da jihar ta saka tare da yunkurin kai wa jami'an gwamnati hari.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng