Yanzun-nan: Gwamnan Zamfara ya bayar da umarnin rufe ko ina a jahar saboda coronavirus

Yanzun-nan: Gwamnan Zamfara ya bayar da umarnin rufe ko ina a jahar saboda coronavirus

- Gwamnan Zmfara, Muhammad Matawalle ya yi umurnin rufe duk wasu ofishoshi na gwamnati da ma’aikatu a fadin jahar

- Hakan na daga cikin matakin da gwamnatin jahar ta dauka domin hana yaduwar cutar coronavirus

- Bincike ya nuna cewa Gwamna Bello Muhammad ya kasance a cikin gida tun bayan da ya dawo jahar a ranar Alhamis da ya gabata daga wani tafiya da ya yi zuwa kasar waje

Gwamnatin jahar Zamfara ta rufe duk wasu ofishoshi na gwamnati da ma’aikatu a fadin jahar.

Bincike ya nuna cewa Gwamna Bello Muhammad ya kasance a cikin gida tun bayan da ya dawo jahar a ranar Alhamis da ya gabata daga wani tafiya da ya yi zuwa kasar waje bayan ya dan yada zango a Abuja.

Yanzun-nan: Gwamnan Zamfara ya bayar da umarnin rufe ko ina a jahar saboda coronavirus
Yanzun-nan: Gwamnan Zamfara ya bayar da umarnin rufe ko ina a jahar saboda coronavirus
Asali: UGC

Gwamnan ya halarci wajen duba cibiyar killace mutane na Coronavirus a cibiyar lafiya ta tarayya, Gusau a ranar Juma’a bayan ya dawo jahar.

Uwargidar gwamnan ta Hajiya Aisha Bello Muhammad ta soke wani taron manema labarai a gidan gwamnan da misalin karfe 3:00 na rana, sa’a daya kafin lokacin da aka shirya gudanar da taron.

Kwamishinan yan sandan jahar, Usman Nagoggo ya haramta duk wani taro a fadin kasar sannan ya yi umurnin rage yawan mutane a ofishishin yan sanda, ciki harda sallaman dukkanin masu kananan laifuffuka.

KU KARANTA KUMA: An samu karin sabbin alamomi dake bayyanar da Coronavirus a jikin dan Adam

A wani labari makamancin haka mun ji cewa Gwamnan jahar Neja, Alhaji Abubakar Sani Bello ya sanar da rufe harkoki a jahar, inda ya kaddamar da hana zirga-zirga daga karfe 8:00 na safe zuwa 8:00 na dare.

A cewar gwamnan takaita zirga-zirgan zai fara ne daga ranar Laraba kamar yadda ya sanar a ranar Litinin, 23 ya watan Maris.

Ya ce akwai bukatar daukar wannan mataki sakamakon sabbin mutanen da aka samu sun kamu da cutar Coronavirus a Abuja, wanda jahar Neja ce mafi kusa da birnin tarayyar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng