Babbar magana: An nade kafet din Masallacin Harami a Saudiyya saboda coronavirus

Babbar magana: An nade kafet din Masallacin Harami a Saudiyya saboda coronavirus

A yayinda rahotanni suka bayyana cewa an kara samun karuwar mutane a kalla 19 da suka kamu da kwayar cutar corona a kasar Saudiyya, shugaban masallatan Haramain da ke birnin Makkah da Madinah, Sheikh Sudais, ya bayar da umarnin a nade shinfidun da ke cikin masallatan.

A wata sanarwa da shafin masallatan ya fitar a shafinsa na dandalin sada zumuntar 'facebook' (Haramain Sharifain), an bayyana cewa za an maye gurbin kafet din masallatan da wasu layuka da aka zana a kan tayil din masallatan.

A sanarwar da aka wallafa a shafin, an ga hotunan wasu ma'aikatan masallatan na nade kafet din tare da zana sabbin layukan.

DUBA WANNAN: Coronavirus: Yadda fasinja ya jawo tashin hankula a filin jirgin sama na Legas

Nade shimfidun masallatan na daga cikin matakan kiyaye wa da kare yaduwar kwayar cutar coronavirus da ke cigaba da yaduwa a sassan duniya.

A cikin makon jiya ne hukumomin kasar Saudiyya suka sanar da rufe masallatan Harami da dakatar da aikin Umrah sakamakon bular annobar kwayar cutar corona.

Babbar magana: An nade kafet din Masallacin Harami a Saudiyya saboda coronavirus
An nade kafet din Masallacin Harami a Saudiyya saboda coronavirus
Asali: Facebook

Babbar magana: An nade kafet din Masallacin Harami a Saudiyya saboda coronavirus
Ana nade kafet din Masallacin Harami a Saudiyya saboda coronavirus
Asali: Facebook

Babbar magana: An nade kafet din Masallacin Harami a Saudiyya saboda coronavirus
An nade kafet din Masallacin Harami a Saudiyya saboda coronavirus
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel