Tsohon sarki Sanusi II ya garzaya Kotu

Tsohon sarki Sanusi II ya garzaya Kotu

Tsohon Sarkin Kano da aka sauke daga kan kujerarsa a ranar Litinin, Sanusi Lamido, ya lashi takobin bin hakkinsa a kotu domin kalubalantar tsige shi da kuma kange shi a wani wuri da sunan gudun hijira.

Lauyan sarki Sanusi, Abubakar Mahmoud (SAN), ne ya bayyana hakan da yammacin yau, Talata, yayin gana wa da manema labarai a Abuja.

Lauyan ya ce sauke Sanusi da tsare shi a wata mafaka sun saba wa doka tare da take hakkinsa na bil'adama.

A ranar Litinin ne gwamnatin Kano, ta bakin Usman Alhaji, sakataren gwamnatin jiha, ta sanar da sauke Sanusi II daga kujerar sarkin Kano bisa zarginsa da rashin biyayya ga sabbin dokokin masarautun jihar Kano da aka kirkira a karshen shekarar 2019.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng