Abinda Sheikh Dahiru Bauchi ya fada a kan tube Sanusi II (sautin murya)
A yayin da jama'a ke cigaba da bayyana mabanbantan ra'ayoyi a kan tsige Muahammadu Sanusi II daga kujerar sarkin Kano, babban malamin darikar Tijjaniya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya tofa albarkacin bakinsa.
A wata tattaunawa da ya yi da sashen Hausa na radiyon BBC, Sheikh Dahiru Bauchi, ya ce tun bayan samun sanarwar tube Sanusi II, suke aika sako ga magoya bayansu a kan su kwantar da hankalinsu, kar su tashi hankalinsu a kan abinda ya faru.
A cewar, babban malamin, wuta da kudi suna hannun gwamnta, a saboda haka zasu iya daukan mataki marar dadi a kan wadanda suka fito domin nuna rashin jin dadinsu.
Sheikh Dahiru Bauchi ya yi addu'a ga tsohon Sarki Sanusi tare da yi masa fatan alheri a rayuwa.
DUBA WANNAN: Tuna baya: Hotunan sarakuna 7 da aka taba tube wa rawani kamar Sanusi II
"Su suke da wuta a hannusu, su suke da kudi a hannunsu, zasu iya bayar da umarnin a harbe mutane. Babu gwamnati a hannunmu, a saboda haka babu wanda zai saurare mu," a cewar Sheikh Dahiru.
Sannan ya cigaba da cewa, "a kwantar da hankali, kar a tayar da hankali, a cigaba da addu'a, gara a yi shiru, Allah zai yi mana sakayya."
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng