Takaitaccen tarihin kakan Aisha Buhari: Ministan tsaro ma farko a Najeriya

Takaitaccen tarihin kakan Aisha Buhari: Ministan tsaro ma farko a Najeriya

Aisha Buhari ta fito ne daga babban gida na 'yan Boko da suka rike manyan mukamai a gwamnatin Najeriya.

Muhammadu Ribadu, kakan Aisha Buhari, fitaccen dan siyasa ne a yankin arewa da ma Najeriya baki daya.

An nada Muhammadu Ribadu a matsayin ministan tsaro na farko na kasa bayan samun 'yancin kai. An nada shi a matsayin mamba a majalisar kasa a shekarar 1947 kafin daga bisani a sake zabensa a shekarar 1951.

Ya taba zama mamba a hukumar raya harkokin noma ta Najeriya kafin daga baya ya zama mamba a bangaren bayar da rance a hukumar cigaban yankin arewa.

Takaitaccen tarihin kakan Aisha Buhari: Ministan tsaro ma farko a Najeriya
Muhammadu Rubadu
Asali: Twitter

An zabe shi a matsayin wakili a taron sake yi wa kundin tsarin mulki kwaskwarima a garin Ibadan a shekarar 1950.

DUBA WANNAN: Fansho da albashi: SERAP ta fitar da sunayen tsofin gwamnoni da ke cin 'tudu biyu' a asusun Najeriya

A shekarar 1952 ne aka nada shi a matsayin ministan albarkatun kasa. An zabe shi a mata mataimakin shugaban jam'iyyar NPC, mukamin da yasa ake saka shi a cikin jerin manyan shugabannin da suka fito daga arewa irinsu Ahmadu Bello da Tafawa Balewa.

Ya rike mukamin ministan kasa, ma'adanai da lantarki a shekarar 1954, ya zama ministan kasa da harkokin Lagos a shekarar 1959.

An haife shi a shekarar 1910, ya mutu a shekarar 1965, watau yana da shekara 55 a duniya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng