Da duminsa: Firam Ministan Malaysiya, Mahathir Mohamad, yayi murabus

Da duminsa: Firam Ministan Malaysiya, Mahathir Mohamad, yayi murabus

Firam Ministan Malaysiya, Mahathir Mohamad, ya sanar da murabus dinsa daga kujerar domin bada damar da samar da sabuwar gwamnati.

Ya aikewa sarkin Malaysiya wasikar ne a ranar Litinin misalin karfe 1 na rana (Agogon Malaysiya), jawabi daga ofishin firam ministan ya bayyana.

Jima kadan bayan hakan, ya sake murabus matsayin shugaban jamiyyar Parti Pribumi Bersatu Malaysia (Bersatu).

Murabus din Mahathir Mohamed ya baiwa mutane mamaki kuma hakan ya faru ne bayan an fara rade-radin cewa yana kokarin kafa sabuwar gwamnati tsakanin United Malays National Organisation (UMNO), Parti Islam Se-Malaysia (PAS) da sauransu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng