Wasu suna kashe kudinsu ne a kan 'hodar iblis' da luwadi, na zabi sayen motoci - Dino Mekaye ya yi 'shagube'

Wasu suna kashe kudinsu ne a kan 'hodar iblis' da luwadi, na zabi sayen motoci - Dino Mekaye ya yi 'shagube'

Tsohon mamba mai wakiltar jihar Kogi ta yamma a majalisar dattijai, Sanata Dino Melaye, ya ce gara ya kashe kudinsa a kan sayen motoci a kan ya kashe su a kan hodar iblis da luwadi kamar yadda wasu ke yi.

Melaye ya bayyana hakan ne ranar Lahadi a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta bayan wani mawaki, Speed Darlington, ya soke shi.

Tsohon dan majalisar ya kasance mai alfahari da tutiya da motocin alfarma masu tsada da ya mallaka. A cikin hotunan motocinsa da yake yawan daukan hoto tare da su a garejin gidansa, akwai Rolls Royce, Bentley, Mercedes Bez G Class da Ferrari.

Mawaki Darlington ya nuna mamakinsa a kan tarin motocin da Melaye ya mallaka, inda ya bayyana cewa, "ikon Allah! duba tarin dukiyar da mutum daya ya mallaka don kawai ya taba zama sanata a Najeriya. An yi sa'a bai samu nasarar lashe zaben gwamna ba, sun karya kafarsa yayin zabe. Bai kamata wani mutum da bashi da sana'a sai siyasa ba ya mallaki dukiya mai yawa haka".

Wasu suna kashe kudinsu ne a kan 'hodar iblis' da luwadi, na zabi sayen motoci - Dino Mekaye ya yi 'shagube'
Dino Mekaye da motocinsa
Asali: Instagram

Da yake mayar da martani, Melaye ya ce yana sha'awar sayen motoci kuma bai kamata hakan ya zama matsala ga kowa ba.

DUBA WANNAN: An bayyana abinda cire su Buratai zai haifar a Najeriya

"Kowa yana kashe kudinsa ne a kan abinda yake so. Ni burina shine na mallaki motocin kece raini. Masu tsafi suna kashe makudan kudi domin sayen jini. Wasu a kan luwadi suke kashe kudinsu, wasu a kan bokaye, wasu a kan hodar iblis, wasu kuma su je su boye kudinsu a Switzerland," a martanin Melaye.

Melaye, dan jam'iyyar PDP, mamba ne a majalisar dattijai ta 9 kafin kotu ta soke zabena tare da bayar da umarnin sake sabon zabe, wanda ya jam'iyyar APC ta lashe.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel