Hotuna daga taron FEC da shugaba Buhari ya jagoranta
A yau, ranar Laraba, 19 ga watan Fabrairu, ne shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya jagoranci zaman majalisar zartar wa ta tarayya (FEC) wanda aka saba yi kowanne mako.
Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ne yake jagorantar taron FEC idan shugaban kasa ba ya nan.
Taron FEC yana samun halartar ministoci, sakataren gwamnatin tarayya (SGF), shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, shugaban hukumar kula da ma'aikatan gwmnatin tarayya da kuma mai bawa shugaban kasa shawara a kan harkokin tsaro.
Yayin taron, ministoci kan gabatar da kudiri ko yin karin bayani a kan aiyukan da suka shafi ma'aikatunsu tare da bayar da gudunmawarsu a sauran batutuwan kasa da ake tattauna wa yayin taron.
Taron, wanda shine kwatankwacin irin na bangaren masu kirkira doka, watau 'yan majalisar tarayya, ana gudanar da shine kowacce ranar Laraba domin bawa bangaren zartarwa damar tattauna batutuwan da suka shafi cigaban kasa.
DUBA WANNAN: Ibrahim Ibrahim: Dan Najeriya da aka yanke wa hukuncin kisa a kasar Saudiyya ya samu 'yanci
Bangaren zartarwa kan yi amfani da taron wajen amincewa da muhimman aiyukan da gwamnatin tarayya zata yi a sassan kasa ko kuma sake duba a kan wasu aiyukan da gwamnati ke gudanar wa.

Asali: Twitter

Asali: Twitter

Asali: Twitter

Asali: Twitter
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng