Allah ya yiwa wani tsohon dan majalisa rasuwa jim kadan bayan kammala bikin zagayowar ranar haihuwarsa

Allah ya yiwa wani tsohon dan majalisa rasuwa jim kadan bayan kammala bikin zagayowar ranar haihuwarsa

- Allah ya yiwa sohon shugaban masu rinjaye a majalisar dokokin jihar Ogun, Hon. Yinka Mafe rasuwa

- Marigayin ya mutu ne a daren ranar Talata, jim kadan bayan bikin cikarsa shekara 46

- Mafe ya yi korafin ciwon kirji bayan bikin inda ya mutu daga bisani

Tsohon shugaban masu rinjaye a majalisar dokokin jihar Ogun, Hon. Yinka Mafe, ya mutu.

An tattaro cewa ya mutu ne a daren ranar Talata, jim kadan bayan bikin cikarsa shekara 46.

Mafe ya yi korafin ciwon kirji bayan bikin inda ya mutu daga bisani.

An ajiye gawarsa a wajen ajiye gawa na asibitin koyarwa na jami’ar Olabisi Onabanjo (OOUTH).

Asiwaju Yinka Mafe wanda aka haifa a ranar 4 ga watan Fabrairu, 1974, ya yi kansilan unguwa uku a karamar hukumar Sagamu a Disamba 1998, wa’adin da ya kare a 2002.

Allah ya yiwa wani tsohon dan majalisa rasuwa jim kadan bayan kammala bikin zagayowar ranar haihuwarsa
Allah ya yiwa wani tsohon dan majalisa rasuwa jim kadan bayan kammala bikin zagayowar ranar haihuwarsa
Asali: UGC

Ya wakilci mazabar mazabar Sagamu a majalisr dokokin jiha tsakanin 2011 da 2019 a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC), wacce ta kasance Action Congress of Nigeria (ACN) a baya.

A farkon ranar Talata, Mafe ya shirya taron addu’a a gidansa da ke Emuren don bikin zagayowar ranar haihuwarsa.

KU KARANTA KUMA: Kurunkus: Nathaniel Samuel ya fadi sunan wacce ta tura shi cikin coci da bam (Bidiyo)

An tattaro cewa ya ziyarci fursunoni a cibiyar gyaran halayya, Sagamu kafin bikin zagayowar ranar wanda aka yi a Tenth Planet and Suite a Sagamu wanda ya damu halartan mutane da dama.

A wani labari na daban, mun ji cewa hukumar kashe gobara ta jahar Zamfara ta sanar tare da tabbatar da tashin gobara a gidan wani dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Gusau/Tsafe, Alhaji Kabiru Mai Palace, dake garin Gusau a ranar Talata.

Kamfanin dillancin labarun Najeriya, NAN, ta ruwaito mataimakin darakta a hukumar, Abdullahi Jibo ne ya bayyana haka yayin da yake ganawa da wakilinta, inda yace wutar ta tashi ne a gidan dake unguwar Yarima, cikin garin Gusau.

Malam Jibo yace alamu sun nuna wutar lantarki ne ya yi sanadiyyar tashin gobarar, saboda a cewarsa da misalin karfe 10:30 na safiyar talata suka samu kiranye daga unguwar game da tashin gobarar, inda yace ba tare da bata lokaci ba jami’ansu suka isa gidan, suka kuma kashe wutar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel