Buhari ya nada tsohon gwarzon dan kwallon kafa, Daniel Amokachi, a matsayin jakada

Buhari ya nada tsohon gwarzon dan kwallon kafa, Daniel Amokachi, a matsayin jakada

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya amince da nada tsohon gwarzon dan wasa kuma mataimakin kociyan kungiyar kwallon kafa ta kasa, 'Super Eagles', Daniel Amokachi, a matsayin jakadan kwallon kafa na Najeriya.

Amokachi ya taka muhimmiyar rawa a kungiyar 'Super Eagles' a lokacin da ta samu nasarar lashe gasar cin kofin kasashen nahiyar Afrika a shekarar 1994 da 1996, shekarar da Najeriya ta samu nasarar lashe zinare a gasar 'Atlanta Olympics'.

Tsohon gwarzon dan wasan ya taka leda a kungiyar kwallon kafa ta 'Everton' da ke kasar Ingila, inda ya kai ga samun nasarar lashe kofin FA tare da kuniyar a shekarar 1995. Bayan ya yi ritaya, Amokachi ya zama mai horar wa a kungiyar kwallon kafa ta jihar Nasarawa kafin daga bisani ya rike kungiyar kwallon kafa ta Enyimba da ke garin Aba.

Buhari ya nada tsohon gwarzon dan kwallon kafa, Daniel Amokachi, a matsayin jakada
Daniel Amokachi
Asali: Getty Images

A matsayinsa na jakadan kwallon kafa na Najeriya, duk da mukami ne na girmamawa kawai, Amokachi zai bawa gwamnatin tarayya gudunmawa a ma'aikatar matasa da wasanni musamman a bangaren zakulo masu hazaka da baiwar iya taka leda, inganta harkokin kungiyar kwallon kafa ta kasa da kuma bayar da shawarwari ga matasa, maza da mata, a kan harkokin motsa jiki.

DUBA WANNAN: Abinda Buhari ya fada wa Lawan da Gbajabiamila a kan tsaro yayin ganawarsu

An haifi Amokachi a ranar 30 ga watan Disamba na shekarar 1972 a garin Kaduna. Mahaifinsa, Ikwulechin Amokachi, dan asalin garin Otukpa ne ta karamar hukumar Ogbadibo a jihar Benuwe.

Amokachi ya taka leda a kungiyar 'Super Eagles' tare da fitattun 'yan wasan kwallon kafa da suka hada da; Jay Jay Okocha, Sunday Oluseh, Samson Sia Sia da sauransu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng