Hukumar yaki da cin hanci ta Kano ta kama ma'ajin fadar sarki Sanusi
A wani labari da Legit.ng taci karo da shi a shafin Salihu Tanko Yakasai, daya daga cikin hadiman gwamnan jihar Kano, hukumar yaki da cin hanci da rasha wa ta Kano ta kama ma'ajin fadar Kano bisa zargin tafka badakala.
A takaitaccen sakon da Yakasai ya wallafa a shafinsa na Tuwita (@dawisu) ya bayyana cewa, "hukumar yaki da cin hanci ta Kano ta kama ma'ajin fadar sarkin Kano a kan sayar da wani fili da fadar Kano tayi ba bisa ka'ida ba,".
Hukumar yaki da cin hanci ta Kano a karkashin shugabancin Muhyi Magaji Rimin Gado ta dade tana binciken fadar sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, a kan zargin tafka badakala da almubazzaranci da kudaden fadar.
Sai dai, wasu da dama na ganin cewa binciken da hukumar ke yi wa fadar ba zai rasa nasaba da tsamin da dangantaka ta yi a tsakanin fadar da gwamnatin jihar ba.
DUBA WANNAN: Wani mutum ya yi fim din batsa a arewacin Najeriya da 'yammata da matan aure
Yakasai bai bayyana a kan wanne fili ne hukumar yai da cin hancin ta kama Ma'ajin ba. Kazalika, bai bayar da cikakken bayani a kan lamarin ba.
Legit.ng zata kawo karin bayani da zarar ta samu.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng