An kai harin makami mai linzami ofishin jakadanci Amurka dake Baghdad

An kai harin makami mai linzami ofishin jakadanci Amurka dake Baghdad

Wani labari da dumi - duminsa da Legit.ng ta samu daga shafin 'Spectator Index' dake shafin Tuwita ya bayyana cewa an sake kai harin makamin roka mai linzami a kan ofishin jakadancin kasar Amurka dake Baghdad, babban birnin kasar Iraqi.

A cikin takaitaccen sakon da 'Spectator Index' ta wallafa, an bayyana cewa harin ya lalata wani bangare na ofishin jakadanci da ake cin abinci.

"Da duminsa: An kai harin makamin roka mai linzami a ofishin jakadancin kasar Amurka dake Baghdad a yau, an lalata bangaren cin abinci," a cewar 'Spectator Index'.

Ya zuwa yanzu, babu wata kungiya ko kasa data dauki alhakin kai harin, kazalika, babu rahoton asarar rai.

Ko a ranar 12 ga watan Janairu saida aka kai wasu munanan harin rokoki sansanin sojin Balad da sojojin kasar Amurka ke zaune a birnin Baghdad na kasar Iraqi, kamar yadda jami'an tsaro suka tabbatar.

A wancan lokacin, AFP ta ruwaito cewa sojojin Amurka sun arce daga sansanin yayin da sojojin kasar Iraqi hudu suka jikkata a harin.

An kai harin makami mai linzami ofishin jakadanci Amurka dake Baghdad
Baghdad
Asali: Facebook

Wani jami'in dan sanda a yankin, Salah-Al-Din, ya bayana cewa rokokin sun dira cikin sansanin sojojin saman.

A farkon watan Janairu ne kasar Iran ta harba rokoki masu linzami guda zuwa 20 sansanin sojojin Amurka dake Iraqi domin mayar da martani a kan kisan babban hafsan rundunar sojojin Iran, Qassem Soleimani, da Amurka ta yi.

DUBA WANNAN: An yi fim din batsa da 'yammata da matan aure a arewacin Najeriya

An harba rokokin ne zuwa sansanin Ayn Al Asad da Sansanin Erbil Asad da misalin karfe 5:30 na yamma, kuma da alamun a kalla sojojin Amurka 80 sun hallaka, a cewar wasu rahotanni.

Amma Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya ce babu dan Amurkan ko daya da ya samu rauni a harin da Iran ta kai sansanin Sojin Amurka dake Iraqi.

Trump ya yi kira ga kasashen Turai, Rasha, Sin, Jamus da Ingila a kan su fita daga yarjejeniyar nukiliya da suka shiga a shekarar 2015.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng