An kai harin makami mai linzami ofishin jakadanci Amurka dake Baghdad

An kai harin makami mai linzami ofishin jakadanci Amurka dake Baghdad

Wani labari da dumi - duminsa da Legit.ng ta samu daga shafin 'Spectator Index' dake shafin Tuwita ya bayyana cewa an sake kai harin makamin roka mai linzami a kan ofishin jakadancin kasar Amurka dake Baghdad, babban birnin kasar Iraqi.

A cikin takaitaccen sakon da 'Spectator Index' ta wallafa, an bayyana cewa harin ya lalata wani bangare na ofishin jakadanci da ake cin abinci.

"Da duminsa: An kai harin makamin roka mai linzami a ofishin jakadancin kasar Amurka dake Baghdad a yau, an lalata bangaren cin abinci," a cewar 'Spectator Index'.

Ya zuwa yanzu, babu wata kungiya ko kasa data dauki alhakin kai harin, kazalika, babu rahoton asarar rai.

Ko a ranar 12 ga watan Janairu saida aka kai wasu munanan harin rokoki sansanin sojin Balad da sojojin kasar Amurka ke zaune a birnin Baghdad na kasar Iraqi, kamar yadda jami'an tsaro suka tabbatar.

A wancan lokacin, AFP ta ruwaito cewa sojojin Amurka sun arce daga sansanin yayin da sojojin kasar Iraqi hudu suka jikkata a harin.

An kai harin makami mai linzami ofishin jakadanci Amurka dake Baghdad
Baghdad
Asali: Facebook

Wani jami'in dan sanda a yankin, Salah-Al-Din, ya bayana cewa rokokin sun dira cikin sansanin sojojin saman.

A farkon watan Janairu ne kasar Iran ta harba rokoki masu linzami guda zuwa 20 sansanin sojojin Amurka dake Iraqi domin mayar da martani a kan kisan babban hafsan rundunar sojojin Iran, Qassem Soleimani, da Amurka ta yi.

DUBA WANNAN: An yi fim din batsa da 'yammata da matan aure a arewacin Najeriya

An harba rokokin ne zuwa sansanin Ayn Al Asad da Sansanin Erbil Asad da misalin karfe 5:30 na yamma, kuma da alamun a kalla sojojin Amurka 80 sun hallaka, a cewar wasu rahotanni.

Amma Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya ce babu dan Amurkan ko daya da ya samu rauni a harin da Iran ta kai sansanin Sojin Amurka dake Iraqi.

Trump ya yi kira ga kasashen Turai, Rasha, Sin, Jamus da Ingila a kan su fita daga yarjejeniyar nukiliya da suka shiga a shekarar 2015.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel