Wani attajiri a Najeriya zai kawar da sauro har abada

Wani attajiri a Najeriya zai kawar da sauro har abada

Ned Nwoko, tsohon dan majalisar tarayya mai wakiltar jihar Delta ta Arewa a majalisar wakilai, ya ce ya shirya tsaf da matuka jirgin da za su yi wa Najeriya feshi gabadaya.

A yayin zantawa da manema labarai a ranar Litinin a filin sauka da tashin jiragen sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, Nwoko ya ce feshi ne kadai zai kawo karshen sauro a kasar nan tare da tabbatar da fatattakar cutar Malaria ta har abada.

Kamar yadda wani rubutu da aka wallafa a shafinsa na kan shi ya bayyana, za a dau nauyin jami'o'i biyar a nahiyar Afirka da za su yi bincike don habaka riga-kafin cutar zazzabin cizon sauro, kamar yadda jaridar The Cable ta ruwaito.

"Gidauniyar Ned Nwoko ta shirya tsaf don fatattakar cutar zazzabin cizon sauro a nahiyar Afirka kafin shekarar 2030," rubutun da aka wallafa ya ce.

DUBA WANNAN: Rashawa: Ba zan sassauta wa Abubakar ba - Gwamnan Bauchi

"Mataki na farko na cimma hakan shi ne feshi a Najeriya da sauran kasashen Afirka don kawo karshen sauro a Afirka. Don cimma wannan manufa, za a yi taro da masu ruwa da tsaki kuma za a nada jakadai da jami'ai don hakan." in ji gidauniyar

"Mataki na biyu kuwa shine kirkiro da hanyar kirkiro riga-kafin cutar zazzabin cizon sauron. Gidauniyar Ned Nwoko za ta dau nauyin binciken riga-kafin cutar zazzabin cizon sauro a manyan jami'o'i biyar na nahiyar Afirka." ta kara da cewa.

Nwoko wanda cikin kwanakin nan ya nufa Antarctica, ya ce ya zabi nan ne don ya jawo hankali a kan yakin korar zazzabin cizon sauro a Najeriya da Afirka.

"Babban aiki ne da muka shirya tabbatar da shi. Zaku iya tunanin cewa Najeriya ta yi girman da ba za a iya yi mata feshi ba amma zamu yi kuma za ku gani," in ji shi.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164