Mun karbi hukuncin kotun koli da zuciya daya – APC Adamawa

Mun karbi hukuncin kotun koli da zuciya daya – APC Adamawa

- Jam'iyyar APC reshen jihar Adamawa ta bayyana cewa ta amince da hukuncin kotun koli da zuciya daya

- Kotun koli ta tabbatar da zaben Gwamna Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP a ranar Talata

- Jam'iyyar ta APC ta kuma yi godiya ga dukkanin wadanda suka mara mata baya a shari’arta har zuwa matakin kotun koli

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) reshen jihar Adamawa ta bayyana cewa ta amince da hukuncin kotun koli da zuciya daya.

Kotun kolin a ranar Talata ta tabbatar da zaben Gwamna Ahmadu Fintiri na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), ta kuma yi watsi da karar APC da dan takararta a zaben gwamnan da ya gabata, Mohammed Jibrilla Bindow, wanda ya kasance gwamna a lokacin da aka gudanar da zaben.

A wani jawabi daga sakatarenta, Mohammed Abdullahi, jam’iyyar ta taya tsohon gwamna Bindow, masu ruwa da tsaki, zababbun yan Majalisar wakilai, da masu yiwa jam’iyyar biyayya jaje a kan hukuncin kotun kolin, amma ta bukaci da su kwantar da hankalinsu.

KU KARANTA KUMA: Abdulmumin Jibrin ya saduda, yana neman sulhu da shugabannin APC gabannin zaben da za a sake (bidiyo)

Ya yi godiya ga dukkanin wadanda suka mara wa jam’iyyar baya a shari’arta har zuwa matakin kotun koli.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng