Sanata Nazif ya ce babu makawa sai PDP ta kwato kujarar Shugaban kasa a 2023

Sanata Nazif ya ce babu makawa sai PDP ta kwato kujarar Shugaban kasa a 2023

Mataimakin Shugaban jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) na kasa a arewa, Sanata Suleiman Muhammad Nazif, ya bayyana cewa jam’iyyar za ta kwato kujerar shugaban kasa sannan ta lashe mafi rinjaye na jihohin arewa a zaben 2023.

Nazif ya ce gwamnatin APC mai mulki ta ba yan Najeriya kunya da tsarin shugabancinta a kasar, don haka sun yanke shawarar tsige jam’iyyar a zabe mai zuwa.

Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, 23 ga watan Janairu a wani sakon taya murna zuwa ga gwamnonin Adama, Ahmadu Fintiri; Taraba, Ishaku Darius; Bauchi, Sanata Bala Mohammed; Benue, Samuel Ortom da Sokoto, Aminu Tambuwal wadanda suka yi nasarar a shari’an kwanan nan da kotun koli ta yanke.

Ya ce koda dai an yiwa jam’iyyar fashin nasarorinta a zaben da ya gabata, ta yi nasarar kwato wasu jihohi da ta rasa a 2015.

Sanatan ya kuma bayar da tabbacin cewa PDP za ta kawo karin jihohi daga arewa a karkashin jagorancinsa a 2023, inda ya bukaci yan Najeriya da su yi Imani da jam’iyyar sannan su yi aiki ya hadin kai da cigaban ta.

KU KARANTA KUMA: Yan bindiga na kashe mutanena a kullun ba tare da gwamnati ta dauki mataki ba – Sanata Sani Musa

Da ya ke korafi kan faduwar jam’iyyar a jihohin Gombe, Plateau da Kano a zaben 2019, ya yi kira ga dukkanin magoya bayan jam’iyyar da su ajiye banbanci sannan su yi aiki don hadin kai da ingancin jam’iyyar domin kawo sauyi a kasar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng